< Romawa 4 >

1 To, me za mu ce Ibrahim kakan kakanninmu ya gani game da wannan batu?
اَسْماکَں پُورْوَّپُرُشَ اِبْراہِیمْ کایِکَکْرِیَیا کِں لَبْدھَوانْ ایتَدَدھِ کِں وَدِشْیامَح؟
2 In fa da gaske ne Ibrahim ya sami kuɓuta ta wurin ayyuka, yana da abin da zai yin taƙama da shi ke nan, amma ba a gaban Allah ba.
سَ یَدِ نِجَکْرِیابھْیَح سَپُنْیو بھَویتْ تَرْہِ تَسْیاتْمَشْلاگھاں کَرْتُّں پَنْتھا بھَویدِتِ سَتْیَں، کِنْتْوِیشْوَرَسْیَ سَمِیپے نَہِ۔
3 Me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
شاسْتْرے کِں لِکھَتِ؟ اِبْراہِیمْ اِیشْوَرے وِشْوَسَناتْ سَ وِشْواسَسْتَسْمَے پُنْیارْتھَں گَنِتو بَبھُووَ۔
4 To, sa’ad da mutum ya yi aiki, ba a lissafta ladan aikinsa a matsayin kyauta, sai dai a matsayin hakkinsa.
کَرْمَّکارِنو یَدْ ویتَنَں تَدْ اَنُگْرَہَسْیَ پھَلَں نَہِ کِنْتُ تینوپارْجِتَں مَنْتَوْیَمْ۔
5 Amma fa, game da mutumin da ba ya aiki sai dai dogara ga Allah wanda yake kuɓutar da masu mugunta, akan lissafta bangaskiyarsa a matsayin adalci ne.
کِنْتُ یَح پاپِنَں سَپُنْیِیکَروتِ تَسْمِنْ وِشْواسِنَح کَرْمَّہِینَسْیَ جَنَسْیَ یو وِشْواسَح سَ پُنْیارْتھَں گَنْیو بھَوَتِ۔
6 Dawuda ya faɗi haka sa’ad da ya yi magana game da albarkar da aka yi wa mutumin da Allah ya lissafta adalci a gare shi, ba don yă yi ayyuka ba.
اَپَرَں یَں کْرِیاہِینَمْ اِیشْوَرَح سَپُنْیِیکَروتِ تَسْیَ دھَنْیَوادَں دایُودْ وَرْنَیاماسَ، یَتھا،
7 “Masu albarka ne waɗanda aka gafarta laifofinsu, waɗanda aka kuma rufe zunubansu.
سَ دھَنْیوگھانِ مرِشْٹانِ یَسْیاگاںسْیاورِتانِ چَ۔
8 Mai albarka ne mutumin da Ubangiji ba zai taɓa lissafta zunubansa ba.”
سَ چَ دھَنْیَح پَریشینَ پاپَں یَسْیَ نَ گَنْیَتے۔
9 Shin, wannan albarkar a kan masu kaciya ne kawai, ko kuwa har da marasa kaciya ma? Mun sha faɗi cewa an lissafta bangaskiyar Ibrahim adalci ne a gare shi.
ایشَ دھَنْیَوادَسْتْوَکْچھیدِنَمْ اَتْوَکْچھیدِنَں وا کَں پْرَتِ بھَوَتِ؟ اِبْراہِیمو وِشْواسَح پُنْیارْتھَں گَنِتَ اِتِ وَیَں وَدامَح۔
10 A kan wane hali ne aka lissafta masa? Bayan da aka yi masa kaciya ne, ko kuwa kafin kaciyar? Ba bayan an yi masa kaciya ba ne, amma kafin a yi masa kaciya!
سَ وِشْواسَسْتَسْیَ تْوَکْچھیدِتْواوَسْتھایاں کِمْ اَتْوَکْچھیدِتْواوَسْتھایاں کَسْمِنْ سَمَیے پُنْیَمِوَ گَنِتَح؟ تْوَکْچھیدِتْواوَسْتھایاں نَہِ کِنْتْوَتْوَکْچھیدِتْواوَسْتھایاں۔
11 Ya kuma karɓi alamar kaciya, hatimin adalcin da yake da shi ta wurin bangaskiya tun yana marar kaciya. Saboda haka fa, ya zama mahaifin dukan waɗanda suka gaskata domin su ma a lasafta su masu adalci ne, ba tare da an yi musu kaciya ba.
اَپَرَنْچَ سَ یَتْ سَرْوّیشامْ اَتْوَکْچھیدِناں وِشْواسِنامْ آدِپُرُشو بھَویتْ، تے چَ پُنْیَوَتّوینَ گَنْییرَنْ؛
12 Ya kuma zama mahaifin masu kaciya waɗanda ba kaciya kaɗai suke da ita ba amma har ma suna bin gurbin bangaskiyar da mahaifinmu Ibrahim yake da ita kafin aka yi masa kaciya.
یے چَ لوکاح کیوَلَں چھِنَّتْوَچو نَ سَنْتو سْمَتْپُورْوَّپُرُشَ اِبْراہِیمْ اَچھِنَّتْوَکْ سَنْ یینَ وِشْواسَمارْگینَ گَتَوانْ تینَیوَ تَسْیَ پادَچِہْنینَ گَچّھَنْتِ تیشاں تْوَکْچھیدِنامَپْیادِپُرُشو بھَویتْ تَدَرْتھَمْ اَتْوَکْچھیدِنو مانَوَسْیَ وِشْواساتْ پُنْیَمْ اُتْپَدْیَتَ اِتِ پْرَمانَسْوَرُوپَں تْوَکْچھیدَچِہْنَں سَ پْراپْنوتْ۔
13 Ba ta wurin doka ce Ibrahim da zuriyarsa suka sami alkawarin cewa zai zama magājin duniya ba, amma sai dai ta wurin adalcin da yake zuwa ta wurin bangaskiya.
اِبْراہِیمْ جَگَتودھِکارِی بھَوِشْیَتِ یَیشا پْرَتِجْنا تَں تَسْیَ وَںشَنْچَ پْرَتِ پُورْوَّمْ اَکْرِیَتَ سا وْیَوَسْتھامُولِکا نَہِ کِنْتُ وِشْواسَجَنْیَپُنْیَمُولِکا۔
14 Gama da a ce masu kiyaye doka ne magāda, ai, da bangaskiya ba ta da amfani, alkawarin kuma ya zama banza,
یَتو وْیَوَسْتھاوَلَمْبِنو یَدْیَدھِکارِنو بھَوَنْتِ تَرْہِ وِشْواسو وِپھَلو جایَتے سا پْرَتِجْناپِ لُپْتَیوَ۔
15 domin doka tana jawo fushi ne. Kuma inda babu doka babu keta umarni ke nan.
اَدھِکَنْتُ وْیَوَسْتھا کوپَں جَنَیَتِ یَتو وِدْیَمانایاں وْیَوَسْتھایامْ آجْنالَنْگھَنَں نَ سَمْبھَوَتِ۔
16 Saboda haka, alkawari yakan zo ta wurin bangaskiya ne, domin yă zama ta wurin alheri, don a tabbatar wa dukan zuriyar Ibrahim ba kawai ga waɗanda suke na doka ba amma har ma ga waɗanda suke na bangaskiyar Ibrahim. Shi ne kuwa mahaifinmu duka.
اَتَایوَ سا پْرَتِجْنا یَدْ اَنُگْرَہَسْیَ پھَلَں بھَویتْ تَدَرْتھَں وِشْواسَمُولِکا یَتَسْتَتھاتْوے تَدْوَںشَسَمُدایَں پْرَتِ اَرْتھَتو یے وْیَوَسْتھَیا تَدْوَںشَسَمْبھَواح کیوَلَں تانْ پْرَتِ نَہِ کِنْتُ یَ اِبْراہِیمِییَوِشْواسینَ تَتْسَمْبھَواسْتانَپِ پْرَتِ سا پْرَتِجْنا سْتھاسْنُرْبھَوَتِ۔
17 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Na mai da kai uban al’ummai masu yawa.” Shi ubanmu ne a gaban Allah, wanda a cikinsa ya gaskata, Allahn da yake ba da rai ga matattu, yake kuma kiran abubuwan da ba su kasance ba su zama kamar sun kasance.
یو نِرْجِیوانْ سَجِیوانْ اَوِدْیَمانانِ وَسْتُونِ چَ وِدْیَمانانِ کَروتِ اِبْراہِیمو وِشْواسَبھُومیسْتَسْییشْوَرَسْیَ ساکْشاتْ سوسْماکَں سَرْوّیشامْ آدِپُرُشَ آسْتے، یَتھا لِکھِتَں وِدْیَتے، اَہَں تْواں بَہُجاتِینامْ آدِپُرُشَں کرِتْوا نِیُکْتَوانْ۔
18 Saɓanin dukan bege, Ibrahim cikin bege ya gaskata, haka kuwa ya zama uban al’ummai masu yawa, kamar yadda aka riga aka faɗa masa cewa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
تْوَدِییَسْتادرِشو وَںشو جَنِشْیَتے یَدِدَں واکْیَں پْرَتِشْرُتَں تَدَنُسارادْ اِبْراہِیمْ بَہُدیشِییَلوکانامْ آدِپُرُشو یَدْ بھَوَتِ تَدَرْتھَں سونَپیکْشِتَوْیَمَپْیَپیکْشَمانو وِشْواسَں کرِتَوانْ۔
19 Ba tare da ya bar bangaskiyarsa ta yi rauni ba, ya fuskanci gaskiyan nan mai cewa jikinsa mai tsufa matacce ne, da yake yana da shekara wajen ɗari, mahaifar Saratu kuma matacciya ce.
اَپَرَنْچَ کْشِینَوِشْواسو نَ بھُوتْوا شَتَوَتْسَرَوَیَسْکَتْواتْ سْوَشَرِیرَسْیَ جَراں سارانامْنَح سْوَبھارْیّایا رَجونِورِتِّنْچَ ترِنایَ نَ مینے۔
20 Duk da haka bai yi shakka ta wurin rashin bangaskiya game da alkawarin Allah ba, sai ma ya ƙara ƙarfafa ga bangaskiyarsa, ya kuma ɗaukaka Allah,
اَپَرَمْ اَوِشْواسادْ اِیشْوَرَسْیَ پْرَتِجْناوَچَنے کَمَپِ سَںشَیَں نَ چَکارَ؛
21 yana kuma da cikakken tabbaci cewa Allah yana da iko yă cika abin da ya yi alkawari.
کِنْتْوِیشْوَرینَ یَتْ پْرَتِشْرُتَں تَتْ سادھَیِتُں شَکْیَتَ اِتِ نِشْچِتَں وِجْنایَ درِڈھَوِشْواسَح سَنْ اِیشْوَرَسْیَ مَہِمانَں پْرَکاشَیانْچَکارَ۔
22 Shi ya sa, “aka lissafta adalci a gare shi.”
اِتِ ہیتوسْتَسْیَ سَ وِشْواسَسْتَدِییَپُنْیَمِوَ گَنَیانْچَکْرے۔
23 Kalmomin nan, “aka lissafta a gare shi” ba a rubuta su saboda shi kaɗai ba ne,
پُنْیَمِواگَنْیَتَ تَتْ کیوَلَسْیَ تَسْیَ نِمِتَّں لِکھِتَں نَہِ، اَسْماکَں نِمِتَّمَپِ،
24 amma saboda mu ma, mu da Allah zai lissafta adalci, mu da muka ba da gaskiya gare shi da ya tashe Yesu Ubangijinmu daga matattu.
یَتوسْماکَں پاپَناشارْتھَں سَمَرْپِتوسْماکَں پُنْیَپْراپْتْیَرْتھَنْچوتّھاپِتوبھَوَتْ یوسْماکَں پْرَبھُ رْیِیشُسْتَسْیوتّھاپَیِتَرِیشْوَری
25 An miƙa shi ga mutuwa saboda zunubanmu, aka kuma tashe shi zuwa rai saboda Allah zai same mu marasa laifi.
یَدِ وَیَں وِشْوَسامَسْتَرْہْیَسْماکَمَپِ سَایوَ وِشْواسَح پُنْیَمِوَ گَنَیِشْیَتے۔

< Romawa 4 >