< Romawa 12 >

1 Saboda haka, ina roƙonku,’yan’uwa, saboda yawan jinƙan Allah, ku miƙa jikunanku hadaya wadda take mai rai, mai tsarki abin karɓa kuma ga Allah, wannan ita ce hanyar hidimarku ta ruhaniya.
Jeg formaner eder altså, brødre, ved Guds miskunn at I fremstiller eders legemer som et levende, hellig, Gud velbehagelig offer - dette er eders åndelige gudstjeneste -
2 Kada ku ci gaba da yin abin da duniya take yi, sai dai ku bar halinku ya sāke, ta wurin sabunta hankalinku ɗungum, don ku tabbatar da abin da Allah yake so yake, abu mai kyau, mai daɗi da kuma cikakke. (aiōn g165)
og skikk eder ikke like med denne verden, men bli forvandlet ved fornyelsen av eders sinn, så I kan prøve hvad som er Guds vilje: det gode og velbehagelige og fullkomne! (aiōn g165)
3 Gama ta wurin alherin nan da aka yi mini ne ina ce wa kowannenku. Kada yă ɗauki kansa fiye da yadda ya kamata, a maimakon haka bari yă auna kansa cikin natsuwa, gwargwadon baiwar bangaskiyar da Allah yi masa.
For ved den nåde som er mig gitt, sier jeg til enhver iblandt eder at han ikke skal tenke høiere enn han bør tenke, men tenke så at han tenker sindig, alt efter som Gud har tilmålt enhver hans mål av tro.
4 Kamar dai yadda kowannenmu yake da jiki ɗaya da gaɓoɓi da yawa, gaɓoɓin nan kuwa ba aiki iri ɗaya suke yi ba,
For likesom vi har mange lemmer på ett legeme, men ikke alle lemmene har samme gjerning,
5 haka ma a cikin Kiristi mu da muke da yawa mun zama jiki ɗaya, kuma kowace gaɓar ɗan’uwan sauran ne.
således er vi mange ett legeme i Kristus, men hver for sig er vi hverandres lemmer.
6 Muna da baye-baye dabam-dabam, gwargwadon alherin da aka yi mana. In baiwar mutum ta yin annabci ce, sai yă yi amfani da ita gwargwadon bangaskiyarsa.
Og da vi har ulike nådegaver, alt efter den nåde som er oss gitt, så la oss, om vi har profetisk gave, bruke den efter som vi har tro til,
7 In ta hidima ce; sai yă yi hidima. In kuma ta koyarwa ce, sai yă koyar;
eller om vi har en tjeneste, ta vare på tjenesten, eller om en er lærer, på lærdommen,
8 in ta ƙarfafawa ce, sai yă ƙarfafa; in kuma ta ba da taimako ce don biyan bukatun waɗansu, sai yă yi haka hannu sake; in ta shugabanci ce, sai yă yi shugabanci da himma; in ta nuna jinƙai ce, sai yă yi haka da fara’a.
eller om en skal formane, på formaningen; den som utdeler, gjøre det med ærlig hu; den som er forstander, være det med iver; den som gjør barmhjertighet, gjøre det med glede!
9 Dole ƙauna tă zama ta gaskiya. Ku ƙi duk abin da yake mugu; ku manne wa abin da yake nagari.
Kjærligheten være uten skrømt; avsky det onde, hold fast ved det gode!
10 Ku ba da kanku ga juna cikin ƙauna irin ta’yan’uwa. Kowa yă yi ƙoƙari wajen girmama wani fiye da kansa.
Vær ømhjertede mot hverandre i broderkjærlighet; kappes om å hedre hverandre!
11 Kada ku zama marasa himma, sai dai masu himma a ruhaniyarku, kuna bauta wa Ubangiji.
Vær ikke lunkne i eders iver; vær brennende i ånden; tjen Herren!
12 Ku yi farin ciki cikin bege, haƙuri cikin shan wuya, aminci cikin addu’a.
Vær glade i håpet, tålmodige i trengselen, vedholdende i bønnen.
13 Ku taimaki mutanen Allah masu bukata. Ku zama masu karɓan baƙi.
Ta eder av de hellige i deres trang; legg vinn på gjestfrihet!
14 Ku sa wa masu tsananta muku albarka; ku sa albarka kada fa ku la’anta.
Velsign dem som forfølger eder; velsign, og forbann ikke!
15 Ku yi murna da masu murna, ku yi kuka da masu kuka.
Gled eder med de glade, og gråt med de gråtende!
16 Ku yi zaman lafiya da juna. Kada ku nuna girman kai, sai ma ku riƙa cuɗanya da talakawa. Kada ku zama masu ɗaga kai.
Ha ett sinnelag mot hverandre; attrå ikke det høie, men hold eder gjerne til det lave; vær ikke selvkloke!
17 Idan kowa ya yi muku mugunta, kada ku sāka masa da mugunta. Ku lura don ku aikata abin da kowa zai iya gani cewa daidai ne.
Gjengjeld ikke nogen ondt med ondt; legg vinn på det som godt er, for alle menneskers åsyn!
18 Ku yi iya ƙoƙarinku, in zai yiwu, ku yi zaman lafiya da kowa.
Såfremt det er mulig, da hold I på eders side fred med alle mennesker!
19 Kada ku yi ramuwa, abokaina, sai dai ku bar wa Allah. Gama a rubuce yake cewa, “Ramuwa tawa ce; zan kuwa sāka,” in ji Ubangiji.
Hevn eder ikke selv, mine elskede, men gi vreden rum! for det er skrevet: Mig hører hevnen til, jeg vil gjengjelde, sier Herren.
20 A maimakon haka, “In abokin gābanka yana jin yunwa, ka ciyar da shi; in yana jin ƙishirwa, ka ba shi ruwan sha. Ta yin haka, za ka tara garwashin wuta a kansa.”
Om da din fiende hungrer, så gi ham å ete; om han tørster, gi ham å drikke! for når du gjør dette, sanker du gloende kull på hans hode.
21 Kada ku bar mugunta ta sha kanku, sai dai ku sha kan mugunta ta wurin aikata nagarta.
La dig ikke overvinne av det onde, men overvinn det onde med det gode!

< Romawa 12 >