< 1 Korintiyawa 1 >
1 Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
Paulus, ved Guds vilje kalt til Kristi Jesu apostel, og broderen Sostenes
2 Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
- til den Guds menighet som er i Korint, helligede i Kristus Jesus, kalte, hellige, tillikemed alle dem som på ethvert sted påkaller vår Herre Jesu Kristi navn, deres og vår:
3 Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Nåde være med eder og fred fra Gud vår Fader og den Herre Jesus Kristus!
4 Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
Jeg takker alltid min Gud for eder, for den Guds nåde som er eder gitt i Kristus Jesus,
5 Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
at I i ham er gjort rike på alt, på all lære og all kunnskap,
6 gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
likesom Kristi vidnesbyrd er blitt rotfestet i eder,
7 Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
så at det ikke fattes eder på nogen nådegave mens I venter på vår Herre Jesu Kristi åpenbarelse,
8 Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
han som også skal styrke eder inntil enden, så I må være ulastelige på vår Herre Jesu Kristi dag.
9 Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
Gud er trofast, han ved hvem I blev kalt til samfund med hans Sønn, Jesus Kristus, vår Herre.
10 Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
Men jeg formaner eder, brødre, ved vår Herre Jesu Kristi navn at I alle må føre den samme tale, og at det ikke må være splid iblandt eder, men at I må være fast forenet i samme sinn og i samme mening.
11 ’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
For det er av Kloes folk blitt mig fortalt om eder, mine brødre, at det er tretter iblandt eder.
12 Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
Jeg mener dette at enhver av eder sier: Jeg holder mig til Paulus; jeg til Apollos; jeg til Kefas; jeg til Kristus.
13 Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
Er Kristus blitt delt? var det Paulus som blev korsfestet for eder, eller var det til Paulus' navn I blev døpt?
14 Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
Jeg takker Gud at jeg ikke har døpt nogen av eder uten Krispus og Gajus,
15 Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
for at ikke nogen skal si at I blev døpt til mitt navn.
16 (I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
Dog har jeg også døpt Stefanas' hus; ellers vet jeg ikke av at jeg har døpt nogen annen.
17 Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
For Kristus har ikke utsendt mig for å døpe, men for å forkynne evangeliet, ikke med vise ord, for at Kristi kors ikke skulde tape sin kraft.
18 Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
For ordet om korset er vel en dårskap for dem som går fortapt, men for oss som blir frelst, er det en Guds kraft;
19 Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
for det er skrevet: Jeg vil ødelegge de vises visdom, og de forstandiges forstand vil jeg gjøre til intet.
20 Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn )
Hvor er en vismann, hvor er en skriftlærd, hvor er en gransker i denne verden? har ikke Gud gjort verdens visdom til dårskap? (aiōn )
21 Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
For eftersom verden ikke ved sin visdom kjente Gud i Guds visdom, var det Guds vilje ved forkynnelsens dårskap å frelse dem som tror,
22 Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
eftersom både jøder krever tegn og grekere søker visdom,
23 amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
men vi forkynner Kristus korsfestet, for jøder et anstøt og for hedninger en dårskap,
24 amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
men for dem som er kalt, både jøder og grekere, forkynner vi Kristus, Guds kraft og Guds visdom.
25 Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
For Guds dårskap er visere enn menneskene, og Guds svakhet er sterkere enn menneskene.
26 ’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
For legg merke til eders kall, brødre, at ikke mange vise efter kjødet blev kalt, ikke mange mektige, ikke mange høibårne;
27 Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
men det som er dårlig i verden, det utvalgte Gud sig for å gjøre de vise til skamme, og det som er svakt i verden, det utvalgte Gud sig for å gjøre det sterke til skamme,
28 Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
og det som er lavt i verden, og det som er ringeaktet, det utvalgte Gud sig, det som ingenting er, for å gjøre til intet det som er noget,
29 domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
forat intet kjød skal rose sig for Gud.
30 Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
Men av ham er I i Kristus Jesus, som er blitt oss visdom fra Gud og rettferdighet og helliggjørelse og forløsning,
31 Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”
forat, som skrevet er: Den som roser sig, han rose sig i Herren!