< Ru’uya ta Yohanna 7 >

1 Bayan wannan, na ga mala’iku huɗu, a tsaye a kusurwoyi huɗu na duniya, suna tsare iskoki huɗu na duniya, domin su hana wani iska hurawa a bisan ƙasa ko a bisan teku ko a bisa wani itace.
And after this I saw four angels standing on the four corners of the earth, holding the four winds of the earth, that the wind should not blow upon the earth, nor the sea, nor upon any tree.
2 Sai na ga wani mala’ika yana zuwa daga gabas, yana da hatimin Allah mai rai. Ya yi kira da babbar murya wa mala’ikun nan huɗu da aka ba su iko su cuci ƙasa da teku ya ce,
And I saw another angel coming up from the rising of the sun, having the seal of the living God: and he cried with a great voice to the four angels, to whom it was given unto them to hurt the earth and the sea,
3 “Kada ku cuci ƙasa ko teku ko kuma itatuwa sai bayan mun sa hatimi a goshin dukan bayin Allahnmu.”
saying, Hurt not the earth, nor the sea, nor the trees, until we may seal the servants of our God in their foreheads.
4 Sai na ji yawan waɗanda aka sa musu hatimi. Su 144,000 daga dukan kabilan Isra’ila.
And I heard the number of the sealed ones: a hundred and forty-four thousand were sealed out of every tribe of the sons of Israel?
5 Daga kabilar Yahuda mutum 12,000 ne aka sa musu hatimin, daga kabilar Ruben mutum 12,000, daga kabilar Gad mutum 12,000,
Out of the tribe of Judah twelve thousand were sealed; of the tribe of Reuben twelve thousand; out of the tribe of Gad, twelve thousand;
6 daga kabilar Asher mutum 12,000, daga kabilar Naftali mutum 12,000, daga kabilar Manasse mutum 12,000,
of the tribe of Asher, twelve thousand; of the tribe of Napthali, twelve thousand; of the tribe of Manasseh, twelve thousand;
7 daga kabilar Simeyon mutum 12,000, daga kabilar Lawi mutum 12,000, daga kabilar Issakar mutum 12,000,
of the tribe of Simeon, twelve thousand; of the tribe of Levi, twelve thousand; of the tribe of Issachar, twelve thousand;
8 daga kabilar Zebulun mutum 12,000, daga kabilar Yusuf mutum 12,000, daga kabilar Benyamin mutum 12,000.
of the tribe of Zebulun, twelve thousand; of the tribe of Joseph, twelve thousand; of the tribe of Benjamin were sealed twelve thousand.
9 Bayan wannan sai na duba, can a gabana kuwa ga wani taro mai girma, wanda ba mai iya ƙirgawa, daga kowace al’umma, kabila, mutane da kuma harshe, suna tsaye a gaban kursiyin da kuma gaban Ɗan Ragon nan. Suna saye da fararen tufafi suna kuma riƙe da rassan dabino a hannuwansu.
After these things I saw, and behold a great multitude, which no one was able to number, out of every nation, and tribes, and peoples, and tongues, standing before the throne, and before the Lamb, clothed in white robes, and palms in their hands;
10 Suka tā da murya da ƙarfi suna cewa, “Ceto na Allahnmu ne, wanda yake zaune a bisan kursiyi, da kuma na Ɗan Ragon.”
and they are crying with a loud voice, saying, Salvation to our God, the one sitting on the throne, and to the Lamb.
11 Dukan mala’iku suna tsaye kewaye da kursiyin da kuma kewaye da dattawan tare da halittu huɗun nan masu rai. Suka fāɗi da fuskokinsu ƙasa a gaban kursiyin suka kuma yi wa Allah sujada,
And all the angels stood round about the throne, and the elders, and the four living creatures, and fell down before the throne on their faces, and worshiped God,
12 suna cewa, “Amin! Yabo da ɗaukaka, da hikima da godiya da girma da iko da ƙarfi sun tabbata ga Allahnmu har abada abadin. Amin!” (aiōn g165)
saying, Amen: blessing, and glory, and wisdom, and thanksgiving, and honor, and power, and strength, to our God unto the ages of the ages: Amen. (aiōn g165)
13 Sai ɗaya daga cikin dattawan ya tambaye ni ya ce, “Waɗannan da suke saye da fararen tufafi su wane ne, daga ina kuma suka fito?”
And one of the elders responded, to me saying, Who are these who are clothed in white robes, and whence came they?
14 Na amsa na ce, “Ranka yă daɗe, kai ka sani.” Sai ya ce, “Waɗannan su ne waɗanda suka fito daga matsananciyar wahala; sun wanke tufafinsu suka kuma mai da su farare da jinin Ɗan Ragon nan.
And I said unto him, My lord, thou knowest. And he said to me; These are those coming up out of great tribulation, who have washed their robes, and made them white in the blood of the Lamb.
15 Saboda haka, “suna a gaban kursiyin Allah suna masa hidima dare da rana a cikin haikalinsa; kuma wannan mai zaune a kursiyin zai shimfiɗa tentinsa a bisansu.
On account of this they are before the throne of God, and they worship him day and night in his temple, and the one sitting upon the throne will spread his tabernacle over them.
16 ‘Ba za su sāke jin yunwa ba; ba za su kuma sāke jin ƙishirwa ba. Rana ba za tă buga su ba,’ ko kuma kowane irin zafin ƙuna.
And they will never hunger or thirst any more; neither will the sun, or any heat, fall on them:
17 Gama Ɗan Ragon da yake a tsakiyar kursiyin zai zama makiyayinsu; ‘zai bi da su zuwa ga maɓulɓular ruwan rai.’ ‘Allah kuwa zai share dukan hawaye daga idanunsu.’”
because the Lamb in the midst of the throne will shepherdize them, and guide them to the fountains of the waters of life; and God will wipe every tear out of their eyes.

< Ru’uya ta Yohanna 7 >