< Ru’uya ta Yohanna 6 >

1 Na kalli yayinda Ɗan Ragon ya buɗe hatimin farko na hatimai bakwai ɗin nan. Sai na ji ɗaya daga cikin halittu huɗun nan masu rai ya yi magana da murya mai kama da tsawa ya ce, “Zo!”
And I saw when the Lamb opened the first of the seven seals, and I heard one of the four living creatures speaking, like a voice of thunder, Come.
2 Na duba, can kuwa a gabana ga wani farin doki! Mai hawansa yana riƙe da baka, aka kuma ba shi rawani, ya yi sukuwa ya fito kamar mai nasara da ya kutsa don nasara.
And I saw, and behold, a white horse: and the one sitting on him having a bow; and a crown was given unto him: and he went forth conquering, and that he might conquer.
3 Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na biyun, sai na ji halitta mai rai na biyu ya ce, “Zo!”
And when he opened the second seal, I heard the second living creature saying, Come.
4 Sai wani doki ya fito, ja wur. Aka ba wa mai hawansa iko yă ɗauke salama daga duniya yă kuma sa mutane su kashe juna. Aka ba shi babban takobi.
And there went out a red horse: and to him sitting on him it was given to take peace from the earth, and that they shall slay one another: and a great sword was given him.
5 Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na uku, sai na ji halitta mai rai na uku ya ce, “Zo!” Na duba, can a gabana kuwa ga wani baƙin doki! Mai hawansa yana riƙe da abubuwan awo guda biyu a hannunsa.
And when he opened the third seal, I heard the third living creature saying, Come. And I saw; and behold a black horse; and the one sitting on him having a balance in his hand.
6 Sai na ji wani abu mai ƙara kamar wata murya a tsakiyar halittu huɗun nan masu rai tana cewa, “Kwatan alkama don albashin aikin yini, da kuma kwata uku na sha’ir don albashin yini guda, kada kuwa ka ɓata man da ruwan inabi!”
And I heard as it were a voice in the midst of the four living creatures saying, A measure of wheat for a denarion, and three measures of barley for a denarion; and hurt not the oil and the wine.
7 Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na huɗu, sai na ji muryar halitta mai rai na huɗu ya ce, “Zo!”
And when he opened the fourth seal, I heard the voice of the fourth living creature saying, Come.
8 Na duba, can a gabana kuwa ga ƙodaɗɗen doki! An ba wa mai hawansa suna Mutuwa, Hades kuwa yana biye da shi. Aka ba su iko a kan kashi ɗaya bisa huɗu na duniya don su yi kisa da takobi, yunwa da annoba, har ma da namomin jeji na duniya. (Hadēs g86)
And I saw, and behold a livid horse: and the one sitting on him, to him the name was Death, and Hades followed along with him: and power was given unto them over the fourth part of the earth, to slay with the sword, and with famine, and with death, and with the wild beasts of the earth. (Hadēs g86)
9 Sa’ad da ya buɗe hatimi na biyar, sai na ga a ƙarƙashin bagaden rayukan waɗanda aka kashe saboda maganar Allah da kuma shaidar da suka yi.
And when he opened the fifth seal, I saw beneath the altar the souls of those who had been slain on account of the word of God, and the testimony which they had.
10 Suka yi kira da babbar murya suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarki da kuma Mai Gaskiya, sai yaushe za ka shari’anta mazaunan duniya ka kuma ɗauki mana fansar jininmu?”
And they cried with a great voice, saying, How long, O Lord, holy and true, do you not judge and avenge our blood from those who dwell upon the earth?
11 Sai aka ba wa kowannensu farin riga, aka kuma faɗa musu su ɗan jira kaɗan sai an cika adadin abokansu masu hidima da kuma’yan’uwansu waɗanda za a kashe kamar yadda su ma aka kashe su.
And a white robe was given to each of them; and it was said to them, that they should wait a little while, until their fellow-servants and brethren, who are about to be slain as they were should be fulfilled.
12 Ina kallo yayinda ya buɗe hatimi na shida. Sai aka yi babban girgizar ƙasa. Rana ta zama baƙa kamar gwado na gashin akuya, wata kuma gaba ɗaya ya zama ja wur kamar jini,
And I saw when he opened the sixth seal, and there was a great earthquake; and the sun became black as sackcloth of hair, and the full moon became like blood;
13 taurarin sararin sama suka fāffāɗi a ƙasa, kamar yadda ɗanyun’ya’yan ɓaure suke fāɗuwa daga itacen ɓaure sa’ad da iska mai ƙarfi ta jijjiga shi.
and the stars of the heaven fell upon the earth, as a fig-tree casting her unripe figs, when shaken by a mighty wind;
14 Sararin sama kuwa ya janye kamar naɗaɗɗen littafi, ya yi ta naɗewa, aka kuma kawar da kowane dutse da kowane tsibiri daga wurinsa.
and the heaven rolled away as a book is rolled up; and every mountain and island were moved out of their places.
15 Sa’an nan sarakunan duniya, hakimai, jarumawa, masu arziki, masu ƙarfi, da kowane bawa da kuma kowane’yantacce ya ɓoye a cikin koguna da kuma cikin duwatsun tsaunuka.
And the kings of the earth, and the mighty men, and the chiliarchs, and the rich men, and the mighty men, and every slave, and every free man, hid themselves in the caves and in the rocks of the mountains,
16 Suka kira duwatsu da tsaunuka suna cewa, “Ku fāɗi a kanmu ku kuma ɓoye mu daga fuskar wannan mai zama a kan kursiyi da kuma daga fushin Ɗan Ragon nan!
and they say to the mountains and to the rocks, Fall on us, and hide us from the face of the one sitting upon the throne, and the wrath of the Lamb:
17 Gama babbar ranar fushinsu ta zo, wa kuwa zai iya tsayawa?”
because the great day of their wrath has come; and who is able to stand?

< Ru’uya ta Yohanna 6 >