< Ru’uya ta Yohanna 18 >

1 Bayan wannan sai na ga wani mala’ika yana saukowa daga sama. Yana da iko mai girma, aka haskaka duniya da darajarsa.
After these things, I saw another messenger, coming down out of heaven, —having great authority; and, the earth, was illumined with his glory.
2 Ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ta fāɗi! Babilon Mai Girma ta fāɗi. Ta zama gidan aljanu da kuma wurin zaman kowace irin mugun ruhu, wurin zaman kowane irin tsuntsu marar tsabta da mai banƙyama.
And he cried out, with a mighty voice, saying—Fallen! fallen! is Babylon the Great, and hath become a habitation of demons, and a prison of every impure spirit, and a prison of every impure and hated bird;
3 Gama dukan al’ummai sun sha ruwan inabin haukan zinace zinacenta. Sarakunan duniya sun yi zina tare da ita, attajiran duniya kuma sun arzuta da almubazzarancinta.”
Because, by reason [of the wine] of the wrath of her lewdness, have all the nations fallen, and, the kings of the earth, with her, did commit lewdness, and, the merchants of the earth, by reason of the power of her wantonness, waxed rich.
4 Sai na ji wata murya daga sama ta ce, “Ku fita daga cikinta, mutanena, don kada zunubanta su shafe ku, don kada wata annobarta ta same ku;
And I heard another voice out of heaven, saying—Come forth, my people, out of her, —that ye may have no fellowship with her sins, and, of her plagues, that ye may not receive;
5 gama zunubanta sun yi tsororuwa sun kai sama. Allah kuma ya tuna da laifofinta.
because her sins were joined together as far as heaven, and God hath remembered her unrighteous deeds.
6 Ku sāka mata kamar yadda ta sāka muku; ku sāka mata sau biyu na abin da ta yi. Ku dama mata sau biyu na abin da yake cikin kwaf nata.
Render ye unto her, as, she also, rendered, and double [the] double, according to her works, —in the cup wherein she mixed, mix, unto her, double, —
7 Ku ba ta isashen azaba da baƙin ciki kamar daraja da kuma jin daɗin da ta ba wa kanta. A zuciyarta takan yi taƙama, ta ce, ‘Ina zama kamar sarauniya; ni ba gwauruwa ba ce, kuma ba zan taɓa yin makoki ba.’
As much as she glorified herself, and waxed wanton, so much give, unto her, torment and grief: —because, in her heart, she saith—I sit a Queen, and, widow, am I not, and, grief, in nowise shall I see!
8 Saboda haka a rana ɗaya annobarta za su cim mata, mutuwa, makoki da kuma yunwa. Wuta zai cinye ta, gama Ubangiji Allah mai girma ne, wanda yake shari’anta ta.
Therefore, in one day, shall have come her plagues, —death and grief and famine; and, with fire, shall she be burned up; —because, mighty, is the [Lord] God who hath judged her.
9 “Sa’ad da sarakunan duniya da suka yi zina da ita suka kuma yi tarayya cikin jin daɗinta suka ga hayaƙin ƙunarta, za su yi kuka da makoki saboda ita.
And they shall weep and wail over her—shall the kings of the earth who, with her, committed lewdness and waxed wanton, —as soon as they see the smoke of her burning, —
10 Don tsoron ganin azabarta za su tsaya daga nesa, su yi kuka suna cewa, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma. Ya ke Babilon, birni mai iko! Cikin sa’a guda hallakarki ta zo!’
afar off, standing, because of their fear of her torment, saying—Alas! alas! the great city! Babylon, the mighty city! That, in one hour, hath come thy judgment.
11 “Attajiran duniya za su yi kuka su kuma yi makoki a kanta, domin ba wanda yake ƙara sayen kayayyakinsu
And, the merchants of the earth, weep and grieve over her, because, their cargo, no one, buyeth any more:
12 kayayyakin zinariya, azurfa, duwatsu masu daraja da lu’ulu’ai; lallausan lilin, tufa masu ruwan shunayya, siliki da jan tufa; da kowane irin katakai masu ƙanshi da kayayyaki na kowane iri da aka yi da hauren giwa, katakai masu tsada, tagulla, baƙin ƙarfe da dutse mai sheƙi;
cargo of gold, and silver, and precious stone, and pearls, and fine linen, and purple, and silk, and scarlet, and all thyine wood, and every article of ivory, and every article of wood most precious, and of copper, and of iron, and of marble,
13 kayayyakin sinnamon da kayan yaji, na turaren wuta, mur da turare, na ruwan inabi da man zaitun, na gari mai laushi da alkama; shanu da tumaki; dawakai da kekunan doki, da jikuna da kuma rayukan mutane.
and cinnamon, and spice, and incense, and unguent, and frankincense, and wine, and oil, and fine flour, and wheat, and cattle, and sheep, and [cargo] of horses, and of chariots, and of bodies, and lives of men.
14 “Za su ce, ‘Amfanin da kike marmari ya kuɓuce. Dukan arzikinki da darajarki sun ɓace, ba kuwa za a ƙara samunsu ba.’
And, the fruit of the coveting of thy soul, hath departed from thee, and, all things rich and bright, have perished from thee; and, no more, in anywise, for them, shall they seek.
15 Attajiran da suka sayar da waɗannan kayayyaki suka kuma sami arzikinsu daga gare ta za su tsaya daga nesa, cike da tsoron ganin azabarta. Za su yi kuka da makoki
The merchants of these things, who were enriched by her, afar off, shall stand, because of their fear of her torment, weeping, and grieving,
16 su ce, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma, saye da lallausan lilin, shunayya da kuma ja, mai walƙiya da zinariya, duwatsu masu daraja da kuma lu’ulu’ai!
as they say—Alas! alas! the great city! She that was arrayed in fine linen, and purple, and scarlet, and decked with gold, and precious stone, and pearl, —
17 Cikin sa’a guda irin wannan dukiya mai yawa ta hallaka!’ “Duk matuƙan jirgin ruwa, da dukan waɗanda suke tafiya a jirgin ruwa, ma’aikatanta, da duk masu samun abin zama gari daga teku za su tsaya daga nesa.
That, in one hour, hath been laid waste, such great wealth as this! And, every pilot, and every passenger, and mariners, and as many as, by the sea, carry on traffic, afar off did stand,
18 Sa’ad da suka ga hayaƙin ƙunarta, za su yi ihu su ce, ‘An taɓa samun birni kamar wannan babban birnin kuwa?’
and they cried out, seeing the smoke of her burning, saying—What city is like unto the great city?
19 Za su zuba ƙura a kawunansu, da kuka da makoki za su yi ta kururuwa, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma, inda dukan waɗanda suke da jiragen ruwa a teku suka arzuta da ɗumbun dukiyarsa! Cikin sa’a ɗaya ta hallaka!’
And they cast dust upon their heads, and cried out, weeping and grieving, saying—Alas! alas! the great city! Whereby were made rich all that had ships in the sea, by reason of her costliness, —that, in one hour, she hath been laid waste!
20 “Ki yi murna a kanta, ya sama! Ku yi murna, ku tsarkaka! Ku yi murna, ku manzanni da annabawa! Allah ya hukunta shi saboda abin da ya yi muku.”
Be glad over her, thou heaven! And ye saints, and ye apostles, and ye prophets! For that God hath exacted your vindication from her.
21 Sa’an nan wani mala’ika mai ƙarfi ya ɗauki dutse kamar girman babban dutsen niƙa ya jefa cikin teku ya ce, “Da wannan irin giggitawa za a jefar da birnin Babilon mai girma ƙasa, ba za a ƙara ganin ta ba.
And one mighty messenger lifted a stone, as it were a great millstone, and cast it into the sea, saying—Thus, with main force, shall be cast down, Babylon the great city, —and in nowise be found any more;
22 Ba za a ƙara jin ƙarar kiɗin masu garaya da muryar mawaƙa, da na masu bushe-bushe, da na masu busan ƙaho a cikinki ba. Ba za a ƙara samun ma’aikaci na kowace irin sana’a a cikinki kuma ba. Ba za a ƙara jin ƙarar dutsen niƙa a cikinki kuma ba.
And sound of harp-singers, and musicians, and flute-players, and trumpeters, —in nowise be heard in thee any more; and any artisan [of any art], —in nowise be found in thee any more; and sound of millstone, —in nowise be found in thee any more;
23 Hasken fitila ba zai ƙara haskakawa a cikinki ba. Ba za a ƙara jin muryar ango da amarya a cikinki ba. Attajiranki, dā su ne manyan mutanen duniya. Ta wurin sihirinki, dukan ƙasashe sun kauce.
And light of lamp, —in nowise shine in thee any more; and voice of bridegroom and bride, —in nowise be heard in thee any more; because, thy merchants, were the great ones of the earth, because, with thy sorcery, were all the nations deceived:
24 A cikinta aka sami jinin annabawa, da na tsarkaka, da kuma na dukan waɗanda aka kashe a duniya.”
And, in her, blood of prophets and saints, was found, —and of all who had been slain upon the earth.

< Ru’uya ta Yohanna 18 >