< Ru’uya ta Yohanna 18 >

1 Bayan wannan sai na ga wani mala’ika yana saukowa daga sama. Yana da iko mai girma, aka haskaka duniya da darajarsa.
这之后,我看见另一位天使从天而降,他拥有伟大的权力,他的荣耀照亮了大地。
2 Ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ta fāɗi! Babilon Mai Girma ta fāɗi. Ta zama gidan aljanu da kuma wurin zaman kowace irin mugun ruhu, wurin zaman kowane irin tsuntsu marar tsabta da mai banƙyama.
他用强有力的声音呼喊:“伟大的巴比伦倾倒为废墟!她已成为恶魔的住处,各样污灵的庇护所,一和一切不洁可憎之鸟的栖息地。
3 Gama dukan al’ummai sun sha ruwan inabin haukan zinace zinacenta. Sarakunan duniya sun yi zina tare da ita, attajiran duniya kuma sun arzuta da almubazzarancinta.”
因为各国都喝了她淫乱烈怒的酒,喝醉了;地上的君王与她行淫,世上的商人因她的挥霍发了财。”
4 Sai na ji wata murya daga sama ta ce, “Ku fita daga cikinta, mutanena, don kada zunubanta su shafe ku, don kada wata annobarta ta same ku;
我听见天上传来另一个声音,说:“从那城出来吧,我的子民!免得她的罪你们也有分,受她所受的灾难;
5 gama zunubanta sun yi tsororuwa sun kai sama. Allah kuma ya tuna da laifofinta.
因为她罪恶滔天,上帝发现了她的邪恶。
6 Ku sāka mata kamar yadda ta sāka muku; ku sāka mata sau biyu na abin da ta yi. Ku dama mata sau biyu na abin da yake cikin kwaf nata.
她怎样待人,你们也要怎样待她;按照她的行为加倍报应她;按照她的酒杯,将加倍的痛苦调给她。
7 Ku ba ta isashen azaba da baƙin ciki kamar daraja da kuma jin daɗin da ta ba wa kanta. A zuciyarta takan yi taƙama, ta ce, ‘Ina zama kamar sarauniya; ni ba gwauruwa ba ce, kuma ba zan taɓa yin makoki ba.’
就像她对自己的吹嘘和放纵自己的欲望一样,给她的回报也是一样的痛苦和悲伤。。她告诉自己:‘我如女王统治,我不是寡妇,决不会感到悲伤。’
8 Saboda haka a rana ɗaya annobarta za su cim mata, mutuwa, makoki da kuma yunwa. Wuta zai cinye ta, gama Ubangiji Allah mai girma ne, wanda yake shari’anta ta.
因为只需一天,她的灾难必然来到,那就是死亡、悲哀和饥荒;她还要被火中摧毁,因为谴责她的主上帝是有着巨大的能力。
9 “Sa’ad da sarakunan duniya da suka yi zina da ita suka kuma yi tarayya cikin jin daɗinta suka ga hayaƙin ƙunarta, za su yi kuka da makoki saboda ita.
地上的众王跟她一同行邪淫, 骄奢无度,看见焚烧她的烟,就会为她痛哭捶胸。
10 Don tsoron ganin azabarta za su tsaya daga nesa, su yi kuka suna cewa, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma. Ya ke Babilon, birni mai iko! Cikin sa’a guda hallakarki ta zo!’
他们害怕会遭受她所受的痛苦,所以远远站着,说:‘灾难!灾难!灾难降临这伟大的城市巴比伦。只需一小时,您的审判就实行了!’
11 “Attajiran duniya za su yi kuka su kuma yi makoki a kanta, domin ba wanda yake ƙara sayen kayayyakinsu
地上的商人也为她悲哀痛哭,因为没有人再买他们的货物:
12 kayayyakin zinariya, azurfa, duwatsu masu daraja da lu’ulu’ai; lallausan lilin, tufa masu ruwan shunayya, siliki da jan tufa; da kowane irin katakai masu ƙanshi da kayayyaki na kowane iri da aka yi da hauren giwa, katakai masu tsada, tagulla, baƙin ƙarfe da dutse mai sheƙi;
金、银、宝石、珍珠;细麻布、紫色布、丝绸、红色材料;各样香木制品,各样象牙制品,各样贵重木器、铜器、铁器、大理石制品;
13 kayayyakin sinnamon da kayan yaji, na turaren wuta, mur da turare, na ruwan inabi da man zaitun, na gari mai laushi da alkama; shanu da tumaki; dawakai da kekunan doki, da jikuna da kuma rayukan mutane.
肉桂、香料、焚香、乳香;酒、橄榄油、面粉、麦子;牛、羊、马、车、奴仆和囚犯。
14 “Za su ce, ‘Amfanin da kike marmari ya kuɓuce. Dukan arzikinki da darajarki sun ɓace, ba kuwa za a ƙara samunsu ba.’
你失去了最喜爱的甜蜜快乐!一切奢华闪亮的财富都从你那里消失,再也找不到了!
15 Attajiran da suka sayar da waɗannan kayayyaki suka kuma sami arzikinsu daga gare ta za su tsaya daga nesa, cike da tsoron ganin azabarta. Za su yi kuka da makoki
贩卖这些货物、借着她发财的商人,因为害怕会遭受她受的痛苦,就远远地站着。他们哭喊着、悲伤着,说
16 su ce, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma, saye da lallausan lilin, shunayya da kuma ja, mai walƙiya da zinariya, duwatsu masu daraja da kuma lu’ulu’ai!
‘灾难!灾难降临了这伟大城市!她穿着细麻布紫色长袍,佩戴金子、宝石和珍珠的珠宝,
17 Cikin sa’a guda irin wannan dukiya mai yawa ta hallaka!’ “Duk matuƙan jirgin ruwa, da dukan waɗanda suke tafiya a jirgin ruwa, ma’aikatanta, da duk masu samun abin zama gari daga teku za su tsaya daga nesa.
只一小时,所有这些财富竟荡然无存!’每个船长、每个海上旅客和水手、以及每个靠海谋生的,都远远地站着。
18 Sa’ad da suka ga hayaƙin ƙunarta, za su yi ihu su ce, ‘An taɓa samun birni kamar wannan babban birnin kuwa?’
摧毁她的火焰飘出烟,他们看到了,就喊叫说:‘有哪座城能与这伟大的城相比?’
19 Za su zuba ƙura a kawunansu, da kuka da makoki za su yi ta kururuwa, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma, inda dukan waɗanda suke da jiragen ruwa a teku suka arzuta da ɗumbun dukiyarsa! Cikin sa’a ɗaya ta hallaka!’
他们把尘土撒在自己头上,痛哭悲哀,喊着说:‘灾难!因为她的奢侈,灾难打击了这让船主富有的伟大城市!只一小时,她就被摧毁了!’
20 “Ki yi murna a kanta, ya sama! Ku yi murna, ku tsarkaka! Ku yi murna, ku manzanni da annabawa! Allah ya hukunta shi saboda abin da ya yi muku.”
天堂、众信徒、众使徒和众先知,庆祝她所发生的事,因为上帝审判她的方式就像审判你一样。”
21 Sa’an nan wani mala’ika mai ƙarfi ya ɗauki dutse kamar girman babban dutsen niƙa ya jefa cikin teku ya ce, “Da wannan irin giggitawa za a jefar da birnin Babilon mai girma ƙasa, ba za a ƙara ganin ta ba.
一位强大的天使,把一块好像磨石一样的石头举起来,拋入海里,说:“伟大的巴比伦城也会被这暴力拋下去,再也不存在。”
22 Ba za a ƙara jin ƙarar kiɗin masu garaya da muryar mawaƙa, da na masu bushe-bushe, da na masu busan ƙaho a cikinki ba. Ba za a ƙara samun ma’aikaci na kowace irin sana’a a cikinki kuma ba. Ba za a ƙara jin ƙarar dutsen niƙa a cikinki kuma ba.
“你们再也不会听到音乐了,竖琴、歌手、长笛和号角。再也不会有任何行业的工匠在你这里工作。在你身上再也听不到磨坊磨出面粉的声音了。
23 Hasken fitila ba zai ƙara haskakawa a cikinki ba. Ba za a ƙara jin muryar ango da amarya a cikinki ba. Attajiranki, dā su ne manyan mutanen duniya. Ta wurin sihirinki, dukan ƙasashe sun kauce.
你们再也不会有灯的亮光照耀了。你们再也听不到新郎新娘的声音了。你们这些商人领导这个世界,所有国家都因你们的邪术受了迷惑。。
24 A cikinta aka sami jinin annabawa, da na tsarkaka, da kuma na dukan waɗanda aka kashe a duniya.”
在这个城市中,能找到先知、信徒和地上一切被杀之人的血。”

< Ru’uya ta Yohanna 18 >