< Yohanna 8 >

1 Amma Yesu ya tafi Dutsen Zaitun.
但耶稣开始去往橄榄山。
2 Da sassafe ya sāke bayyana a filin haikali, inda dukan mutane suka taru kewaye da shi, sai ya zauna don yă koya musu.
黎明时分,他返回圣殿,坐下来教导身边围坐的众人。
3 Sai malaman dokoki da Farisiyawa suka kawo wata macen da aka kama a zina. Suka sa ta tsaya a gaban taron
宗教老师和法利赛人带来一个妇人,她在通奸之时被抓住,叫她站在众人面前。
4 suka kuma ce wa Yesu, “Malam, an kama wannan mace tana zina.
他们就对耶稣说:“老师,这妇人在通奸的时候被抓住。
5 A cikin Doka Musa ya umarce mu, mu jajjefe irin waɗannan mata. To, me ka ce?”
摩西在律法上的裁决是:我们应该用石头将这样的妇人打死,你觉得呢?”
6 Sun yi wannan tambaya ce don su sa masa tarko, don su sami hanyar zarge shi. Amma Yesu ya sunkuya ya fara rubutu a ƙasa da yatsarsa.
他们这样说,其实是想找到耶稣言语中的把柄来控告他。但耶稣却弯下身,用手指在地上写字。
7 Da suka ci gaba da yin masa tambayoyi, sai ya miƙe tsaye ya ce musu, “In da wani a cikinku da ba shi da zunubi, sai yă fara jifanta da dutse.”
他们不停地要求耶稣给出回答。耶稣直起身对他们说:“你们中谁没有罪,谁就可以先拿起石头打她。”
8 Sai ya sāke sunkuyawa ya kuma yi rubutu a ƙasa.
然后他又弯下身在地上写字。
9 Da jin haka, waɗanda suka ji sai suka fara tashi daga wurin ɗaya-ɗaya, tun daga babbansu har ya zuwa ƙaraminsu, sai da aka bar Yesu kaɗai, tare da macen tsaye a wurin.
听到这番话,控诉者中从最年长的那个人开始一个接一个地离开了,,最后人群中只留下耶稣和站在原地的那位妇人。
10 Sai Yesu ya miƙe tsaye ya tambaye ta ya ce, “Mace, ina suke? Ba wanda ya hukunta ki?”
耶稣站直身问她:“他们哪儿去了?没有人留下来定你的罪吗?”
11 Ta ce, “Ba kowa, ranka yă daɗe.” Sai Yesu ya ce, “Haka ni ma ban hukunta ki ba. Ki tafi, ki daina rayuwar zunubi.”
她说:“先生,没有人。” 耶稣说:“我也不会定你的罪。走吧,不要再犯罪了。”
12 Sa’ad da Yesu ya sāke magana da mutanen, sai ya ce, “Ni ne hasken duniya. Duk wanda ya bi ni ba zai yi tafiya cikin duhu ba, sai dai yă sami hasken rayuwa.”
耶稣又对众人说:“我就是这世界的光,如果你跟随我,就不会走进黑暗,因为你将拥有赐予你生命的光。”
13 Sai Farisiyawa suka tambaye shi suka ce, “Ga kai dai, kana yi wa kanka shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.”
法利赛人反驳:“你不能为自己作证!你所说的无法证明任何事!”
14 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, gama na san inda na fito da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ko inda za ni ba.
耶稣告诉他们:“即使我为自己作证,我的证言仍是真实。因为我知道我从哪里来,要到哪里去,但你们却不知道我从哪里来,要到哪里去。
15 Kuna shari’a bisa ga ma’aunin mutane; ni kuwa ba na yin wa kowa shari’a.
你们以人类最常见的方式做出判断,但我不会做出评判。
16 Amma ko da zan yi shari’a, shari’ata daidai ce, don ba ni kaɗai ba ne. Ina tare da Uba da ya aiko ni.
即使我要做出评判,我的判断也是正确的,因为并非一个人在做这件事情,派我前来的天父与我同在。
17 A cikin Dokarku a rubuce yake cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.
你们的律法上也写着:‘两个人的见证才有效。’
18 Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”
我为自己作证,派我前来的天父也为我作证。”
19 Suka tambaye shi suka ce, “Ina Uban nan naka?” Sai Yesu ya ce, “Ba ku san ni ko Ubana ba. Da kun san ni, da za ku san Ubana ma.”
他们问耶稣:“你的父在哪里?”耶稣回答:“你们不认识我或我的天父,如果你们认识我,就会认识我父。”
20 Ya faɗi waɗannan kalmomi ne yayinda yake koyarwa a filin haikali, kusa da inda ake ajiye baye-baye. Duk da haka ba wanda ya kama shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna.
耶稣是在圣殿银库附近教导众人时,做出了这番解释。但没有人逮捕他,因为他的时候尚未到来。
21 Har wa yau Yesu ya sāke ce musu, “Zan tafi, za ku kuwa neme ni, za ku kuma mutu cikin zunubinku. Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba.”
耶稣又对他们说:“我要走了,你们将会寻找我,但你们会因自己的罪而死去,我要去的地方,你们无法抵达。”
22 Wannan ya sa Yahudawa suka yi tambaya suka ce, “Zai kashe kansa ne? Shi ya sa yake cewa, ‘Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba’?”
犹太人思索着,然后大声说:“他要自杀吗?他说‘我要去的地方,你们无法抵达。’是这个意思吗?”
23 Amma ya ci gaba da cewa, “Ku daga ƙasa kuke; ni kuwa daga bisa ne. Ku na duniyan nan ne; ni kuwa ba na duniyan nan ba ne.
耶稣告诉他们:“你们来自人间,我来自天上。你们属于这个世界,我却不属于这世界。
24 Na gaya muku cewa za ku mutu cikin zunubanku; in ba ku gaskata cewa ni ne wanda na ce nake ba, lalle za ku mutu cikin zunubanku.”
所以我对你们说,你们会因自己的罪而死去。因为如果你们不相信我即‘我是’,你们就会因自己的罪而死去。”
25 Suka ce, “Wane ne kai?” Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ne wannan da na sha faɗi muku.
他们又问:“那你到底是谁?” 耶稣回答:“我从一开始就告诉你们的了。
26 Ina da abubuwa masu yawa da zan faɗa game ku in kuma yi muku shari’a. Amma wanda ya aiko ni mai aminci ne, abin da kuma na ji daga gare shi, shi nake gaya wa duniya.”
关于你们,我有很多可以说的,我可以对你们大加谴责,但派我来此的天父讲述的却是真相,我在这个世界对你们所说的,就是从他那里听来的。”
27 Ba su gane cewa yana yin musu magana game da Ubansa ba ne.
他们不明白耶稣所说的就是天父。于是耶稣解释说:
28 Saboda haka Yesu ya ce, “Sa’ad da kuka ɗaga Ɗan Mutum, a sa’an nan ne za ku san cewa ni ne wannan da na ce nake. Ni kuwa ba na yin kome ni kaɗai, sai in dai faɗi abin da Uba ya koya mini.
“如果你们看到人子被高举,必定知道我即‘我是’,知道我的所作所为并非源于自己,我的言语都是遵循天父的教导。
29 Wanda kuwa ya aiko ni yana tare da ni; bai bar ni ni kaɗai ba, domin kullum ina aikata abin da ya gamshe shi.”
那派我来此之人与我同在,他未弃我,因为我的所行皆令其喜悦。”
30 Sa’ad da yake cikin magana, da yawa suka ba da gaskiya gare shi.
很多人在听到耶稣的这番话后,便相信了他。
31 Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
于是耶稣对信他的犹太人说:“你们若遵循我的道,就真正是我的门徒。
32 Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă’yantar da ku.”
你们将知晓真理,真理会让你们自由。”
33 Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a’yantar da mu?”
众人问到:“我们是亚伯拉罕的后裔,从未被奴役过,你说我们会自由,又是何意呢?”
34 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, duk mai yin zunubi bawan zunubi ne.
耶稣答道:“说实话,每个罪人都是罪的奴隶。
35 Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada. (aiōn g165)
奴隶在家庭中无法拥有永远的地位,只有儿子才是家庭中永远的成员。 (aiōn g165)
36 Saboda haka in Ɗan ya’yantar da ku, za ku’yantu da gaske.
当上帝之子让你自由,你就真正获得自由。
37 Na dai san ku zuriyar Ibrahim ne. Duk da haka kuna shiri ku kashe ni, don maganata ba ta da wurin zama a cikinku.
我知道你们是亚伯拉罕的后裔,但你们不愿接收我的道,所以想杀我。
38 Ina faɗi muku abin da na gani a wurin Ubana, ku kuwa kuna yin abin da kuka ji daga wurin ubanku.”
我所说的一切皆为我父显示给我的,但你们只是遵循你们的父亲行事。”
39 Suka ce, “To, ai, Ibrahim ne mahaifinmu.” Yesu ya ce, “Da ku’ya’yan Ibrahim ne, da za ku aikata abubuwan da Ibrahim ya yi.
他们说:“亚伯拉罕就是我们的父亲。” 耶稣说:“你们若真是亚伯拉罕的子孙,就必做亚伯拉罕所行之事。
40 Ga shi kun ƙudura, sai kun kashe ni, ni mutumin da ya faɗa muku gaskiyar da na ji daga Allah. Ibrahim bai yi irin waɗannan abubuwa ba.
但现在,只因我讲述了从上帝那里听见的真理,你们便想杀我,亚伯拉罕绝不会这么做。
41 Kuna yin abubuwan da ubanku yake yi ne.” Suka ce, “Mu fa ba shegu ba ne. Uba guda kaɗai da muke da shi, shi ne Allah kansa.”
你们只是遵循你们的父亲。” 他们回答:“我们不是非法子孙,上帝是我们唯一的父亲。”
42 Yesu ya ce musu, “Da Allah ne Ubanku, da kun ƙaunace ni, gama daga Allah na fito yanzu kuma ga ni nan. Ban zo saboda kaina ba, amma shi ne ya aiko ni.
耶稣说:“如果上帝真是你们的父亲,你们就该爱我,因我来自上帝,现在我就在这里。这不是我的决定,而是派我前来之人的决定。
43 Me ya sa ba kwa gane da maganata? Don ba kwa iya jin abin da nake faɗi.
为什么你们无法理解我的话?因为你们不肯听我所传递的讯息!
44 Ku na ubanku ne, Iblis, kuna kuwa so ku aikata abin da ubanku yake so. Shi mai kisankai ne tun farko. Ba ruwansa da gaskiya, gama gaskiya ba ta cikinsa. Yayinda yake ƙarya, yana yin halinsa ne, gama shi maƙaryaci ne, uban ƙarairayi kuma.
你们的父是魔鬼,你们也喜欢遵循其魔鬼的欲望行事。他从一开始就是杀人犯,不讲真理,因他心里没有真理。当他说谎时便显露了他的本性,因为他就是一个说谎者,是谎言之父。
45 Amma domin ina faɗin gaskiya, ba kwa gaskata!
我说的都是真理,你们却因此而不相信我!
46 Akwai waninku da zai iya haƙaƙƙewa na taɓa yin zunubi? In kuwa gaskiya na faɗa, me ya sa ba kwa gaskata ni?
你们中有谁能指证我有罪?我既然讲真理,你们为什么不信我?
47 Wanda yake na Allah, yakan ji abin da Allah yake faɗi. Abin da ya sa ba kwa jin sa kuwa shi ne don ku ba na Allah ba ne.”
归属于上帝之人就会聆听上帝之语。你们不听,因为你们并不归属于上帝。”
48 Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Aha, ai, gaskiyarmu da muka ce kai mutumin Samariya ne, kana kuma da aljani.”
犹太人对耶稣说:“我们说你是魔鬼附体的撒玛利亚人,难道不对吗?”
49 Yesu ya ce, “Ni ba mai aljani ba ne, ni dai ina girmama Ubana, ku kuwa ba kwa girmama ni.
耶稣回答:“我不是魔鬼附体。我尊敬我父,你们却侮辱我。
50 Ba na nema wa kaina ɗaukaka, amma akwai wani wanda yake neman mini, shi ne kuma alƙali.
我来此并非追求自己的荣耀,但确有一人为我寻求荣耀,来此对人做出审判。
51 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya kiyaye maganata, ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam.” (aiōn g165)
告诉你们实话,遵守我的教导将永远不会死去。” (aiōn g165)
52 Da jin haka Yahudawa suka ce, “Tabɗi, yanzu kam mun san kana da aljani! Ibrahim ya mutu haka ma annabawa, ga shi kana cewa duk wanda ya kiyaye maganarka ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam. (aiōn g165)
犹太人对他说:“现在我们知道你的确是魔鬼附身。亚伯拉罕死了,先知们也死了,你居然还说‘遵守我的教导将永远不会死去’, (aiōn g165)
53 Ka fi Ibrahim mahaifinmu ne? Ya mutu, haka ma annabawa. Wa kake ɗauka kanka ne?”
难道你比我们的祖先亚伯拉罕还伟大吗?他死了,先知们也死了,你把自己当做什么人呢?”
54 Yesu ya amsa ya ce, “In ma na ɗaukaka kaina, ɗaukakata ba kome ba ce. Ubana, wanda kuke cewa shi ne Allahnku, shi ne wanda yake ɗaukaka ni.
耶稣回答:“如果我只获得自己的荣耀,那荣耀就不值一提;让我荣耀之人是上帝,正如你们所说的‘他就是上帝’。
55 Ko da yake ba ku san shi ba, ni dai na san shi. In kuwa na ce ban san shi ba, na zama maƙaryaci kamar ku ke nan, amma na san shi, kuma ina kiyaye maganarsa.
你们不认识他,我却认识。如果我说不认识他,就会像你们一样说谎。但我的确认识他,也遵守他的道。
56 Mahaifinku Ibrahim ya yi farin ciki sosai yă sami ganin ranata; ya kuwa gan ta, ya yi murna.”
你们的祖先亚伯拉罕,因为期待我降临的日子而充满喜悦。当看到指示便感到如此幸福。”
57 Sai Yahudawa suka ce masa, “Kai, shekarunka har yanzu ba su kai hamsin tukuna ba fa, har ka ga Ibrahim!”
犹太人回答:“你还不到五十岁,怎会见过亚伯拉罕呢?”
58 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, tun ba a haifi Ibrahim ba, ni ne!”
耶稣说:“告诉你们实话,亚伯拉罕出生以前,我就已存在。”
59 Da jin haka sai suka ɗebo duwatsu don su jajjefe shi, amma Yesu ya ɓuya, ya fita daga filin haikali.
于是他们捡起石头要去砸他。耶稣躲开他们,离开了圣殿。

< Yohanna 8 >