< Ru’uya ta Yohanna 13 >
1 Macijin kuwa ya tsaya a bakin teku. Sai na ga wata dabba tana fitowa daga teku. Tana da ƙahoni goma da kawuna bakwai, da kuma rawani goma a ƙahoninta, a kowane kai kuwa akwai sunan saɓo.
And he stood on the sand of the sea. And I saw a beast coming up out of the sea, having ten horns and seven heads. On his horns were ten crowns, and on his heads, blasphemous names.
2 Dabbar da na gani ta yi kamar damisa, amma tana da ƙafafu kamar na beyar, bakinta kuma ya yi kamar na zaki. Macijin nan ya ba wa dabbar ƙarfinsa da gadon sarautarsa da kuma ikonsa mai girma.
The beast which I saw was like a leopard, and his feet were like those of a bear, and his mouth like the mouth of a lion. The serpent gave him his power, his throne, and great authority.
3 Ɗaya daga cikin kawunan dabbar ya yi kamar yana da raunin da zai iya kashe shi, amma raunin nan da zai iya kashe shi ya riga ya warke. Dukan duniya ta yi mamaki ta kuma bi dabbar.
One of his heads looked like it had been wounded fatally. His fatal wound was healed, and the whole earth was amazed and followed the beast.
4 Mutane suka yi wa macijin sujada domin ya ba wa dabbar ikonsa, suka yi wa dabbar sujada, suka kuma yi tambaya cewa, “Wane ne yake kama da dabban nan? Wa zai iya yaƙe ta?”
They worshiped the serpent, because he gave his authority to the beast, and they worshiped the beast, saying, "Who is like the beast? Who is able to make war with him?"
5 Aka ba wa dabbar baki don ta faɗi kalmomin girman kai da na saɓo ta kuma yi amfani da ikonta har watanni arba’in da biyu.
A mouth was given to him speaking proud words and blasphemies. There was given to him authority to act for forty-two months.
6 Ta buɗe bakinta don tă yi wa Allah saɓo, ta kuma ɓata sunansa da kuma mazauninsa da na waɗanda suke zama a sama.
He opened his mouth for blasphemies against God, to blaspheme his name, and his dwelling, those who dwell in heaven.
7 Aka ba ta iko tă yaƙi tsarkaka tă kuma ci nasara a kansu. Aka kuma ba ta iko bisa kowace kabila, jama’a, harshe da kuma al’umma.
It was given to him to make war with the saints, and to overcome them. Authority over every tribe, people, language, and nation was given to him.
8 Dukan mazaunan duniya za su yi wa dabbar sujada, dukan waɗanda ba a rubuta sunayensu a cikin littafin ran da yake na Ɗan Ragon da aka yanka tun kafin halittar duniya ba.
All who dwell on the earth will worship him, everyone whose name has not been written from the foundation of the world in the Book of Life of the Lamb who has been killed.
9 Duk mai kunne ji, bari yă ji.
If anyone has an ear, let him hear.
10 Duk wanda aka ƙaddara ga bauta, ga bauta zai tafi. Duk wanda aka ƙaddara za a kashe da takobi, da takobin za a kashe shi. Wannan yana bukata haƙuri da aminci a gefen tsarkaka.
If anyone is to go into captivity, he will go into captivity. If anyone is to be killed with the sword, he must be killed with the sword. Here is the endurance and the faith of the saints.
11 Sai na ga wata dabba tana fitowa daga ƙasa. Tana da ƙahoni biyu kamar ɗan rago, amma ta yi magana kamar maciji.
I saw another beast coming up out of the earth. He had two horns like a lamb, and he spoke like a serpent.
12 Ta mori dukan ikon dabban nan ta fari a madadinta, ta sa duniya da mazaunanta su yi wa dabba ta farin nan sujada, wadda aka warkar mata da raunin nan da zai iya kashe ta.
He exercises all the authority of the first beast in his presence. He makes the earth and those who dwell in it to worship the first beast, whose fatal wound was healed.
13 Ta kuma yi manyan ayyuka da kuma alamu masu banmamaki, har ta sa wuta ta sauko daga sama zuwa ƙasa a gaban idon mutane.
He performs great signs, even making fire come down out of heaven to the earth in the sight of people.
14 Saboda alamun nan da aka ba ta iko tă yi a madadin dabban nan ta fari, sai ta ruɗi mazaunan duniya. Ta umarce su su kafa siffa don girmama dabbar da aka ji mata rauni da takobi duk da haka ta rayu.
He deceives those who dwell on the earth because of the signs he was granted to do in front of the beast; saying to those who dwell on the earth, that they should make an image to the beast who had been wounded by the sword and yet lived.
15 Aka ba ta iko tă ba da numfashi ga siffar dabban nan ta fari, don tă yi magana tă kuma sa a kashe duk waɗanda suka ƙi yi wa siffar sujada.
It was given to him to give breath to it, to the image of the beast, that the image of the beast could both speak and cause those who would not worship the image of the beast to be killed.
16 Ta kuma tilasta wa kowa, manya da yara, mawadata da matalauta,’yantattu da bayi, don a yi musu alama a hannun dama ko a goshi,
He causes all, the small and the great, the rich and the poor, and the free and the slave, to be given a mark on their right hand, or on their forehead;
17 don kada kowa yă saya ko yă sayar, sai dai yana da alamar, wadda take sunan dabbar ko kuma lambar sunanta.
and that no one could be able to buy or to sell, unless he has that mark, the name of the beast or the number of his name.
18 Wannan yana bukata hikima. Duk mai hankali, sai yă lissafta lambar dabbar, gama lamban nan ta mutum ne. Lambarta kuwa ita ce 666.
Here is wisdom. He who has understanding, let him calculate the number of the beast, for it is the number of a man. His number is six hundred sixty-six.