< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
En salme, en sang til sabbatsdagen. Det er godt å prise Herren og å lovsynge ditt navn, du Høieste,
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
å kunngjøre din miskunnhet om morgenen og din trofasthet om nettene
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
til tistrenget citar og til harpe, til tankefullt spill på citar.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
For du har gledet mig, Herre, med ditt verk, jeg jubler over dine henders gjerninger.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
Hvor store dine gjerninger er, Herre! Såre dype er dine tanker.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
En ufornuftig mann kjenner det ikke, og en dåre forstår ikke dette.
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
Når de ugudelige spirer som gresset, og alle de som gjør urett, blomstrer, så er det til deres ødeleggelse for evig tid.
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
Men du er høi til evig tid, Herre!
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
For se, dine fiender, Herre, for se, dine fiender forgår; alle de som gjør urett, blir adspredt.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
Og du ophøier mitt horn som villoksens; jeg er overgytt med frisk olje.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
Og mitt øie ser med fryd på mine motstandere; mine ører hører med glede om de onde som står op imot mig.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
Den rettferdige spirer som palmen; som en seder på Libanon vokser han.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
De er plantet i Herrens hus, de blomstrer i vår Guds forgårder.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Enn i gråhåret alder skyter de friske skudd; de er frodige og grønne
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
for å kunngjøre at Herren er rettvis, han, min klippe, og at det ikke er urett i ham.

< Zabura 92 >