< Zabura 86 >

1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
oratio ipsi David inclina Domine aurem tuam et exaudi me quoniam inops et pauper sum ego
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
custodi animam meam quoniam sanctus sum salvum fac servum tuum Deus meus sperantem in te
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
miserere mei Domine quoniam ad te clamabo tota die
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
laetifica animam servi tui quoniam ad te Domine animam meam levavi
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
quoniam tu Domine suavis et mitis et multae misericordiae omnibus invocantibus te
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
auribus percipe Domine orationem meam et intende voci orationis meae
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
in die tribulationis meae clamavi ad te quia exaudisti me
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
non est similis tui in diis Domine et non est secundum opera tua
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
omnes gentes quascumque fecisti venient et adorabunt coram te Domine et glorificabunt nomen tuum
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
quoniam magnus es tu et faciens mirabilia tu es Deus solus
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
deduc me Domine in via tua et ingrediar in veritate tua laetetur cor meum ut timeat nomen tuum
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
confitebor tibi Domine Deus meus in toto corde meo et glorificabo nomen tuum in aeternum
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol h7585)
quia misericordia tua magna est super me et eruisti animam meam ex inferno inferiori (Sheol h7585)
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
Deus iniqui insurrexerunt super me et synagoga potentium quaesierunt animam meam et non proposuerunt te in conspectu suo
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
et tu Domine Deus miserator et misericors patiens et multae misericordiae et verax
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
respice in me et miserere mei da imperium tuum puero tuo et salvum fac filium ancillae tuae
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
fac mecum signum in bono et videant qui oderunt me et confundantur quoniam tu Domine adiuvasti me et consolatus es me

< Zabura 86 >