< Zabura 86 >

1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
Requête de David. Eternel, écoute, réponds-moi; car je suis affligé et misérable.
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
Garde mon âme, car je suis un de tes bien-aimés; ô toi mon Dieu, délivre ton serviteur, qui se confie en toi.
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Seigneur, aie pitié de moi, car je crie à toi tout le jour.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Réjouis l'âme de ton serviteur; car j'élève mon âme à toi, Seigneur.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
Parce que toi, ô Eternel! es bon et clément, et d'une grande bonté envers tous ceux qui t'invoquent.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Eternel, prête l'oreille à ma prière, et sois attentif à la voix de mes supplications.
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
Je t'invoque au jour de ma détresse, car tu m'exauces.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
Seigneur, il n'y a aucun entre les dieux qui soit semblable à toi, et il n'y a point de telles œuvres que les tiennes.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
Seigneur, toutes les nations que tu as faites viendront, et se prosterneront devant toi, et glorifieront ton Nom;
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
Car tu es grand, et tu fais des choses merveilleuses, tu es Dieu, toi seul.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Eternel! enseigne-moi tes voies, et je marcherai en ta vérité; lie mon cœur à la crainte de ton Nom.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
Seigneur mon Dieu, je te célébrerai de tout mon cœur, et je glorifierai ton Nom à toujours.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol h7585)
Car ta bonté est grande envers moi, et tu as retiré mon âme d'un sépulcre profond. (Sheol h7585)
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
Ô Dieu! des gens orgueilleux se sont élevés contre moi, et une bande de gens terribles, qui ne t'ont point eu devant leurs yeux, a cherché ma vie.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
Mais toi, Seigneur, tu es le [Dieu] Fort, pitoyable, miséricordieux, tardif à colère, et abondant en bonté et en vérité.
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
Tourne-toi vers moi, et aie pitié de moi; donne ta force à ton serviteur, délivre le fils de ta servante.
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
Montre-moi quelque signe de ta faveur, et que ceux qui me haïssent le voient, et soient honteux, parce que tu m'auras aidé, ô Eternel! et m'auras consolé.

< Zabura 86 >