< 2 Tarihi 7 >

1 Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
Et sitôt que Salomon eut achevé de faire sa prière, le feu descendit des cieux, et consuma l'holocauste et les sacrifices, et la gloire de l'Eternel remplit le Temple.
2 Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
Et les Sacrificateurs ne pouvaient entrer dans la maison de l'Eternel, parce que la gloire de l'Eternel avait rempli sa maison.
3 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
Et tous les enfants d'Israël voyant comment le feu descendait, et comment la gloire de l'Eternel était sur la maison, se courbèrent le visage en terre sur le pavé, et se prosternèrent, et célébrèrent l'Eternel, [en disant]: Ô! qu'il est bon, parce que sa gratuité demeure éternellement.
4 Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Or le Roi et tout le peuple sacrifiaient des sacrifices devant l'Eternel.
5 Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
Et le Roi Salomon offrit un sacrifice de vingt et deux mille bœufs, et de six vingt mille brebis. Ainsi le Roi et tout le peuple dédièrent la maison de Dieu.
6 Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
Et les Sacrificateurs se tenaient à leurs emplois, et les Lévites avec les instruments de musique de l'Eternel, que le Roi David avait faits pour célébrer l'Eternel, [en disant], que sa gratuité demeure éternellement; ayant les Psaumes de David entre leurs mains. Les Sacrificateurs aussi sonnaient des trompettes vis-à-vis d'eux, et tout Israël était debout.
7 Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
Et Salomon consacra le milieu du parvis qui était devant la maison de l'Eternel; car il offrit là les holocaustes, et les graisses des sacrifices de prospérités, parce que l'autel d'airain, qu'il avait fait, ne pouvait contenir les holocaustes, et les gâteaux, et les graisses.
8 Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
En ce temps-là donc Salomon célébra une fête solennelle, pendant sept jours, et avec lui, tout Israël, qui était une fort grande multitude de peuple, assemblé depuis Hamath, jusqu'au torrent d'Egypte.
9 A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
Et au huitième jour ils firent une assemblée solennelle, car ils célébrèrent la dédicace de l'autel pendant sept jours, et la fête solennelle, pendant sept autres jours.
10 A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
Et au vingt et troisième jour du septième mois il laissa aller le peuple en ses tentes, se réjouissant et ayant le cœur plein de joie, à cause du bien que l'Eternel avait fait à David, et à Salomon, et à Israël son peuple.
11 Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
Salomon donc acheva la maison de l'Eternel, et la maison Royale; et il réussit en tout ce qu'il avait eu dessein de faire dans la maison de l'Eternel, et dans sa maison.
12 sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
L'Eternel s'apparut encore à Salomon de nuit, et lui dit: J'ai exaucé ta prière, et je me suis choisi ce lieu-ci pour une maison de sacrifice.
13 “Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
Si je ferme les cieux, et qu'il n'y ait point de pluie; et si je commande aux sauterelles de consumer la terre; et si j'envoie la mortalité parmi mon peuple;
14 in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
Et que mon peuple, sur lequel mon Nom est réclamé, s'humilie, et fasse des prières, et recherche ma face, et se détourne de sa mauvaise voie, alors je l'exaucerai des cieux, et je pardonnerai leurs péchés, et je guérirai leur pays.
15 Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
Mes yeux seront désormais ouverts, et mes oreilles attentives à la prière qu'on fera dans ce lieu-ci.
16 Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
Car j'ai maintenant choisi et sanctifié cette maison, afin que mon Nom y soit à toujours; et mes yeux et mon cœur seront toujours-là.
17 “Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
Et quant à toi, si tu marches devant moi comme a marché David ton père, faisant tout ce que je t'ai commande, et [si] tu gardes mes statuts et mes ordonnances;
18 zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
Alors j'affermirai le trône de ton Royaume, comme je l'ai promis à David ton père, en disant: Il ne te sera point retranché de [successeur] pour régner en Israël.
19 “Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
Mais si vous vous détournez, et si vous abandonnez mes statuts, et mes commandements que je vous ai proposés, et que vous vous en alliez et serviez d'autres dieux, et vous prosterniez devant eux;
20 zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
Je les arracherai de dessus ma terre, que je leur ai donnée, et je rejetterai de devant moi cette maison, que j'ai consacrée à mon Nom, et je ferai qu'elle sera un sujet de raillerie parmi tous les peuples.
21 Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
Et quiconque passera près de cette maison, qui aura été haut élevée, sera étonné, et on dira: Pourquoi l'Eternel a-t-il traité ainsi ce pays, et cette maison?
22 Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”
Et on répondra: Parce qu'ils ont abandonné l'Eternel le Dieu de leurs pères, qui les avait retirés du pays d'Egypte, et qu'ils se sont attachés à d'autres dieux, et se sont prosternés devant eux, et les ont servis, à cause de cela il a fait venir tout ce mal sur eux.

< 2 Tarihi 7 >