< Zabura 85 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ka nuna wa ƙasarka alheri, ya Ubangiji; ka mai da nasarorin Yaƙub.
In finem, filiis Core. Psalmus. [Benedixisti, Domine, terram tuam; avertisti captivitatem Jacob.
2 Ka gafarta laifin mutanenka ka kuma shafe dukan zunubansu. (Sela)
Remisisti iniquitatem plebis tuæ; operuisti omnia peccata eorum.
3 Ka kau da dukan fushinka ka kuma juye daga hasalar fushinka.
Mitigasti omnem iram tuam; avertisti ab ira indignationis tuæ.
4 Ka sāke mai da mu, ya Allah Mai Cetonmu, ka kau da rashin jin daɗinka daga gare mu.
Converte nos, Deus salutaris noster, et averte iram tuam a nobis.
5 Za ka ci gaba da fushi da mu har abada ne? Za ka ja fushinka cikin dukan tsararraki?
Numquid in æternum irasceris nobis? aut extendes iram tuam a generatione in generationem?
6 Ba za ka sāke raya mu ba, don mutanenka su yi farin ciki a cikinka?
Deus, tu conversus vivificabis nos, et plebs tua lætabitur in te.
7 Ka nuna mana ƙaunarka marar ƙarewa, ya Ubangiji, ka kuma ba mu cetonka.
Ostende nobis, Domine, misericordiam tuam, et salutare tuum da nobis.
8 Zan saurari abin da Allah Ubangiji zai faɗa; ya yi alkawarin salama ga mutanensa, tsarkakansa, amma kada su koma ga wauta.
Audiam quid loquatur in me Dominus Deus, quoniam loquetur pacem in plebem suam, et super sanctos suos, et in eos qui convertuntur ad cor.
9 Tabbatacce cetonsa yana kusa da waɗanda suke tsoronsa, don ɗaukakarsa ta zauna a cikin ƙasarmu.
Verumtamen prope timentes eum salutare ipsius, ut inhabitet gloria in terra nostra.
10 Ƙauna da aminci za su sadu; adalci da salama za su yi wa juna sumba.
Misericordia et veritas obviaverunt sibi; justitia et pax osculatæ sunt.
11 Aminci zai ɓulɓulo daga ƙasa, adalci kuma yă duba daga sama.
Veritas de terra orta est, et justitia de cælo prospexit.
12 Ubangiji tabbatacce zai bayar da abin da yake da kyau, ƙasarmu kuwa za tă ba da amfaninta.
Etenim Dominus dabit benignitatem, et terra nostra dabit fructum suum.
13 Adalci na tafiya a gabansa yana shirya hanya domin ƙafafunsa.
Justitia ante eum ambulabit, et ponet in via gressus suos.]

< Zabura 85 >