< Zabura 85 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ka nuna wa ƙasarka alheri, ya Ubangiji; ka mai da nasarorin Yaƙub.
Untuk pemimpin biduan. Mazmur bani Korah. Engkau telah berkenan kepada tanah-Mu, ya TUHAN, telah memulihkan keadaan Yakub.
2 Ka gafarta laifin mutanenka ka kuma shafe dukan zunubansu. (Sela)
Engkau telah mengampuni kesalahan umat-Mu, telah menutupi segala dosa mereka. (Sela)
3 Ka kau da dukan fushinka ka kuma juye daga hasalar fushinka.
Engkau telah menyurutkan segala gemas-Mu, telah meredakan murka-Mu yang menyala-nyala.
4 Ka sāke mai da mu, ya Allah Mai Cetonmu, ka kau da rashin jin daɗinka daga gare mu.
Pulihkanlah kami, ya Allah penyelamat kami, dan tiadakanlah sakit hati-Mu kepada kami.
5 Za ka ci gaba da fushi da mu har abada ne? Za ka ja fushinka cikin dukan tsararraki?
Untuk selamanyakah Engkau murka atas kami dan melanjutkan murka-Mu turun-temurun?
6 Ba za ka sāke raya mu ba, don mutanenka su yi farin ciki a cikinka?
Apakah Engkau tidak mau menghidupkan kami kembali, sehingga umat-Mu bersukacita karena Engkau?
7 Ka nuna mana ƙaunarka marar ƙarewa, ya Ubangiji, ka kuma ba mu cetonka.
Perlihatkanlah kepada kami kasih setia-Mu, ya TUHAN, dan berikanlah kepada kami keselamatan dari pada-Mu!
8 Zan saurari abin da Allah Ubangiji zai faɗa; ya yi alkawarin salama ga mutanensa, tsarkakansa, amma kada su koma ga wauta.
Aku mau mendengar apa yang hendak difirmankan Allah, TUHAN. Bukankah Ia hendak berbicara tentang damai kepada umat-Nya dan kepada orang-orang yang dikasihi-Nya, supaya jangan mereka kembali kepada kebodohan?
9 Tabbatacce cetonsa yana kusa da waɗanda suke tsoronsa, don ɗaukakarsa ta zauna a cikin ƙasarmu.
Sesungguhnya keselamatan dari pada-Nya dekat pada orang-orang yang takut akan Dia, sehingga kemuliaan diam di negeri kita.
10 Ƙauna da aminci za su sadu; adalci da salama za su yi wa juna sumba.
Kasih dan kesetiaan akan bertemu, keadilan dan damai sejahtera akan bercium-ciuman.
11 Aminci zai ɓulɓulo daga ƙasa, adalci kuma yă duba daga sama.
Kesetiaan akan tumbuh dari bumi, dan keadilan akan menjenguk dari langit.
12 Ubangiji tabbatacce zai bayar da abin da yake da kyau, ƙasarmu kuwa za tă ba da amfaninta.
Bahkan TUHAN akan memberikan kebaikan, dan negeri kita akan memberi hasilnya.
13 Adalci na tafiya a gabansa yana shirya hanya domin ƙafafunsa.
Keadilan akan berjalan di hadapan-Nya, dan akan membuat jejak kaki-Nya menjadi jalan.