< Zabura 85 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ka nuna wa ƙasarka alheri, ya Ubangiji; ka mai da nasarorin Yaƙub.
To the Chief Musician. For the Sons of Korah. A Melody. Thou hast accepted, O Yahweh, thy land, Thou hast brought back the captives of Jacob;
2 Ka gafarta laifin mutanenka ka kuma shafe dukan zunubansu. (Sela)
Thou hast taken away, the iniquity of thy people, Thou hast covered, all their sin. (Selah)
3 Ka kau da dukan fushinka ka kuma juye daga hasalar fushinka.
Thou hast withdrawn all thine indignation, Thou hast ceased from the glow of thine anger.
4 Ka sāke mai da mu, ya Allah Mai Cetonmu, ka kau da rashin jin daɗinka daga gare mu.
Restore us, O God of our salvation, And take away thy vexation towards us.
5 Za ka ci gaba da fushi da mu har abada ne? Za ka ja fushinka cikin dukan tsararraki?
To times age-abiding, wilt thou be angry with us? Wilt thou prolong thine anger, from generation to generation?
6 Ba za ka sāke raya mu ba, don mutanenka su yi farin ciki a cikinka?
Wilt not, thou thyself, again give us life, That, thy people, may rejoice in thee.
7 Ka nuna mana ƙaunarka marar ƙarewa, ya Ubangiji, ka kuma ba mu cetonka.
Show us, O Yahweh, thy lovingkindness, And, thy salvation, wilt thou grant us.
8 Zan saurari abin da Allah Ubangiji zai faɗa; ya yi alkawarin salama ga mutanensa, tsarkakansa, amma kada su koma ga wauta.
I will hear, what GOD—Yahweh—will speak, —For he will bespeak prosperity to his people, And to his men of lovingkindness, And to them who return with their heart unto him.
9 Tabbatacce cetonsa yana kusa da waɗanda suke tsoronsa, don ɗaukakarsa ta zauna a cikin ƙasarmu.
Surely, near unto them who revere him, is his salvation, That the Glory, may settle down, in our land.
10 Ƙauna da aminci za su sadu; adalci da salama za su yi wa juna sumba.
Lovingkindness and faithfulness, have met together, Righteousness and prosperity, have kissed each other;
11 Aminci zai ɓulɓulo daga ƙasa, adalci kuma yă duba daga sama.
Faithfulness, out of the earth, doth spring forth, And, righteousness, out of the heavens, hath looked down.
12 Ubangiji tabbatacce zai bayar da abin da yake da kyau, ƙasarmu kuwa za tă ba da amfaninta.
Yahweh himself too, will give us the blessing, And, our land, shall yield her increase.
13 Adalci na tafiya a gabansa yana shirya hanya domin ƙafafunsa.
Righteousness, before him, shall march long, —That he may make, into a way, the steps of its feet.