< Zabura 83 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
Una canción. Un salmo de Asaf. Dios, no guardes silencio. No te quedes callado, y no te quedes quieto, Dios.
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
Porque, he aquí, tus enemigos están agitados. Los que te odian han levantado la cabeza.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
Conspiran con astucia contra tu pueblo. Conspiran contra tus seres queridos.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
“Vamos”, dicen, “destruyámoslos como nación, para que el nombre de Israel no sea más recordado”.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
Porque han conspirado juntos con una sola mente. Forman una alianza contra ti.
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
Las tiendas de Edom y de los ismaelitas; Moab, y los Hagritas;
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebal, Amón y Amalec; Filistea con los habitantes de Tiro;
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
También Asiria se une a ellos. Han ayudado a los hijos de Lot. (Selah)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Haz con ellos lo que hiciste con Madián, como a Sísara, como a Jabín, en el río Cisón;
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
que perecieron en Endor, que se convirtió en estiércol para la tierra.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Haz que sus nobles sean como Oreb y Zeeb, sí, todos sus príncipes como Zebah y Zalmunna,
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
que dijo: “Tomemos posesión de las tierras de pastoreo de Dios”.
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
Dios mío, haz que sean como una planta rodadora, como paja ante el viento.
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
Como el fuego que quema el bosque, como la llama que incendia las montañas,
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
así que persíguelos con tu tempestad, y aterrorízalos con tu tormenta.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Llena sus rostros de confusión, para que busquen tu nombre, Yahvé.
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Que queden desilusionados y consternados para siempre. Sí, que se confundan y perezcan;
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
para que sepan que sólo tú, cuyo nombre es Yahvé, eres el Altísimo sobre toda la tierra.