< Zabura 81 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
Til songmeisteren, etter Gittit; av Asaf. Syng med fagnad for Gud, vår styrke! Ropa med gleda for Jakobs Gud!
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
Set i med song, og lat trumma høyrast, den væne cither med harpa!
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Blås i lur ved nymåne, ved fullmåne på vår høgtidsdag!
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
For det er ei lov for Israel, ein rett for Jakobs Gud.
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
Han sette det til eit vitnemål i Josef då han drog ut gjenom Egyptarland. - Eit mål som eg ikkje kjende, høyrde eg:
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
«Eg løyste hans oksl frå byrdi, hans hender vart frie frå berekorgi.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
I trengsla ropa du, og eg fria deg ut, eg svara deg, løynd i toresky, eg prøvde deg ved Meribavatni. (Sela)
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
Høyr, mitt folk, so vil eg vitna for deg! Israel, gjev du vilde høyra på meg!
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
Det skal ikkje finnast nokon annan gud hjå deg, og du skal ikkje tilbeda ein framand gud.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
Eg er Herren, din Gud, som førde deg upp frå Egyptarland, lat munnen vidt upp, at eg kann fylla honom!
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
Men folket mitt høyrde ikkje på mi røyst, og Israel vilde ikkje lyda meg.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
So let eg deim fara med sitt harde hjarta, at dei kunde ganga i sine eigne råder.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
Gjev mitt folk vilde høyra på meg, gjev Israel vilde vandra på mine vegar!
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
Snart skulde eg då bøygja deira fiendar, eg skulde venda mi hand imot deira motstandarar.
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Dei som hatar Herren, skulde høla honom, og deira tid skulde vara æveleg.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
Og eg skulde føda honom med den beste kveite, og frå berget skulde eg metta deg med honning.»

< Zabura 81 >