< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
Ordtøke av Salomo, son til David, konge yver Israel.
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
Av deim kann ein læra visdom og age og skyna vituge ord.
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
Og få age so ein vert klok, rettferd og rett og rettvisa.
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
Dei kann gjeva dei urøynde klokskap, ungdomen kunnskap og ettertanke -
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
so den vise kann høyra og auka sin lærdom og den vituge verta rådklok.
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
Dei gjev skyn på ordtak og myrke ord, ord frå dei vise og gåtorne deira.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
Otte for Herren er upphav til kunnskap, uvitingar vanvyrder visdom og age.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Høyr etter, son min, når far din deg agar, og kasta’kje frå deg det mor di deg lærer!
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
For det er ein yndeleg krans for ditt hovud, og kjedor kring halsen din.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Son min, når syndarar lokkar deg, samtykk ikkje!
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
Um dei segjer: «Kom med oss! Me vil lura etter blod, setja fella for den skuldlause utan grunn;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
Me vil gløypa deim som helheimen livande, og heile som når dei fer i gravi; (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
Me vinna oss alle slag skattar, og fyller husi våre med rov;
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
du skal få lutskifte saman med oss, alle skal me ha same pungen.» -
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
Son min, gakk ikkje då på vegen med deim, haldt foten din burte frå deira stig!
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
For føterne deira spring til vondt og er snøgge til å renna ut blod.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Men fåfengt breier dei netet for augo på alle fuglar.
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
Dei lurer på sitt eige blod og set eit garn for sitt eige liv.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
So gjeng det kvar som riv til seg med ran, det drep sin eigen herre.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
Vismøyi ropar på gata og lyfter si røyst på torgi.
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
På gatehyrna preikar ho midt i ståket, i porthallar og kring i byen ho talar:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
«Kor lenge vil de fåkunnige elska fåkunna, og kor lenge vil spottarar ha hug til spott, og dårar hata kunnskap?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Snu dykk hit når eg refser! So skal åndi mi fløyma for dykk, og eg skal kunngjera dykk mine ord.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Eg ropa og de vilde ikkje høyra, og ingen agta på at eg rette ut handi,
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
De brydde dykk ei um all mi råd, og ansa ikkje mitt refsings ord,
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
So skal eg då læ når de ulukka fær, eg skal spotta når det som de ræddast kjem,
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
når det de ræddast kjem som eit uver, og uferdi dykkar fer hit som ein storm, når trengsla og naud kjem på dykk.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Då vil eg ikkje svara når de ropar på meg, dei skal naudleita etter meg, men ikkje finna meg.
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Av di dei hata kunnskap og forsmådde otte for Herren,
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
ikkje lydde på mi råd, vanyrde all mi påminning,
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
skal dei eta frukt av si åtferd og verta mette av sine råder.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
For einvisa drep dei einfaldne, og tryggleiken dårarne tyner.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Men den bur trygt, som høyrer på meg, verna um ulukke-rædsla.»

< Karin Magana 1 >