< Zabura 80 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
To victorie; this salm is witnessing of Asaph for lilies. Thou that gouernest Israel, yyue tent; that leedist forth Joseph as a scheep. Thou that sittist on cherubym; be schewid bifore Effraym,
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Beniamyn, and Manasses. Stire thi power, and come thou; that thou make vs saaf.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
God of vertues, turne thou vs; and schewe thi face, and we schulen be saaf.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Lord God of vertues; hou longe schalt thou be wrooth on the preier of thi seruaunt?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Hou longe schalt thou feede vs with the breed of teeris; and schalt yyue drynke to vs with teeris in mesure?
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Thou hast set vs in to ayenseiyng to oure neiyboris; and oure enemyes han scornyde vs.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
God of vertues, turne thou vs; and schewe thi face, and we schulen be saaf.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Thou translatidist a vyne fro Egipt; thou castidist out hethene men, and plauntidist it.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Thou were leeder of the weie in the siyt therof; and thou plauntidist the rootis therof, and it fillide the lond.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
The schadewe therof hilide hillis; and the braunchis therof filliden the cedris of God.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
It streiyte forth hise siouns til to the see, and the generacioun ther of `til to the flood.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Whi hast thou destried the wal therof; and alle men that goen forth bi the weie gaderiden awei the grapis therof?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
A boor of the wode distriede it; and a singuler wielde beeste deuouride it.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
God of vertues, be thou turned; biholde thou fro heuene, and se, and visite this vyne.
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
And make thou it perfit, which thi riythond plauntide; and biholde thou on the sone of man, which thou hast confermyd to thee.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Thingis brent with fier, and vndurmyned; schulen perische for the blamyng of thi cheer.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Thin hond be maad on the man of thi riythond; and on the sone of man, whom thou hast confermed to thee.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
And we departiden not fro thee; thou schalt quykene vs, and we schulen inwardli clepe thi name.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Lord God of vertues, turne thou vs; and schewe thi face, and we schulen be saaf.

< Zabura 80 >