< Zabura 79 >

1 Zabura ta Asaf. Ya Allah, al’ummai sun mamaye gādonka; sun ƙazantar da haikalinka mai tsarki, sun bar Urushalima kufai.
Of Asaph. God, hethene men cam in to thin eritage; thei defouliden thin hooli temple, thei settiden Jerusalem in to the keping of applis.
2 Sun ba da gawawwakin bayinka kamar abinci ga tsuntsayen sararin sama, nama jikin tsarkakanka ga namun jejin duniya.
Thei settiden the slayn bodies of thi seruauntis, meetis to the volatilis of heuenes; the fleischis of thi seyntis to the beestis of the erthe.
3 Sun zubar da jini kamar ruwa ko’ina a Urushalima, kuma babu wani da zai binne matattu.
Thei schedden out the blood of hem, as watir in the cumpas of Jerusalem; and noon was that biriede.
4 Mun zama abin reni ga maƙwabta, abin ba’a da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
We ben maad schenschipe to oure neiyboris; mowynge and scornynge to hem, that ben in oure cumpas.
5 Har yaushe, ya Ubangiji za ka yi ta fushi? Har abada ne? Har yaushe kishinka zai yi ta ƙuna kamar wuta?
Lord, hou longe schalt thou be wrooth in to the ende? schal thi veniaunce be kyndelid as fier?
6 Ka zuba fushinka a kan al’umman da ba su yarda da kai ba, a kan mulkokin da ba sa kira bisa sunanka;
Schede out thin ire in to hethene men, that knowen not thee; and in to rewmes, that clepiden not thi name.
7 gama sun cinye Yaƙub suka lalatar da ƙasar zamansa.
For thei eeten Jacob; and maden desolat his place.
8 Kada ka riƙe zunubai kakanni a kanmu; bari jinƙanka yă zo da sauri yă sadu da mu, gama mun fid da zuciya sarai.
Haue thou not mynde on oure elde wickidnesses; thi mercies bifore take vs soone, for we ben maad pore greetli.
9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, saboda ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka kuma gafarta mana zunubanmu saboda sunanka.
God, oure heelthe, helpe thou vs, and, Lord, for the glorie of thi name delyuer thou vs; and be thou merciful to oure synnes for thi name.
10 Don me al’ummai za su ce, “Ina Allahnsu yake?” A idanunmu, ka sanar wa al’ummai cewa kana ɗaukan fansar jinin bayinka da aka zubar.
Lest perauenture thei seie among hethene men, Where is the God of hem? and be he knowun among naciouns bifore oure iyen. The veniaunce of the blood of thi seruauntis, which is sched out; the weilyng of feterid men entre in thi siyt.
11 Bari nishe-nishen’yan kurkuku su zo gabanka; ta wurin ƙarfin hannunka ka kiyaye waɗanda aka yanke wa hukuncin mutuwa.
Vpe the greetnesse of thin arm; welde thou the sones of slayn men.
12 Ka sāka a cinyoyin maƙwabtanmu sau bakwai zage-zagen da suka yi ta yi maka, ya Ubangiji.
And yelde thou to oure neiyboris seuenfoold in the bosum of hem; the schenschip of hem, which thei diden schenschipfuli to thee, thou Lord.
13 Sa’an nan mu mutanenka, tumakin makiyayarka, za mu yabe ka har abada; daga tsara zuwa tsara za mu yi ta ba da labarin yabonka.
But we that ben thi puple, and the scheep of thi leesewe; schulen knouleche to thee in to the world. In generacioun and in to generacioun; we schulen telle thin heriyng.

< Zabura 79 >