< Zabura 79 >

1 Zabura ta Asaf. Ya Allah, al’ummai sun mamaye gādonka; sun ƙazantar da haikalinka mai tsarki, sun bar Urushalima kufai.
A PSALM OF ASAPH. O God, nations have come into Your inheritance, They have defiled Your holy temple, They made Jerusalem become heaps,
2 Sun ba da gawawwakin bayinka kamar abinci ga tsuntsayen sararin sama, nama jikin tsarkakanka ga namun jejin duniya.
They gave the dead bodies of Your servants [As] food for the birds of the heavens, The flesh of Your saints For the wild beast of the earth.
3 Sun zubar da jini kamar ruwa ko’ina a Urushalima, kuma babu wani da zai binne matattu.
They have shed their blood As water around Jerusalem, And there is none burying.
4 Mun zama abin reni ga maƙwabta, abin ba’a da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
We have been a reproach to our neighbors, A scorn and a derision to our surrounders.
5 Har yaushe, ya Ubangiji za ka yi ta fushi? Har abada ne? Har yaushe kishinka zai yi ta ƙuna kamar wuta?
Until when, O YHWH? Are You angry forever? Your jealousy burns as fire.
6 Ka zuba fushinka a kan al’umman da ba su yarda da kai ba, a kan mulkokin da ba sa kira bisa sunanka;
Pour Your fury on the nations who have not known You, And on kingdoms that have not called on Your Name.
7 gama sun cinye Yaƙub suka lalatar da ƙasar zamansa.
For [one] has devoured Jacob, And they have made his habitation desolate.
8 Kada ka riƙe zunubai kakanni a kanmu; bari jinƙanka yă zo da sauri yă sadu da mu, gama mun fid da zuciya sarai.
Do not remember for us the iniquities of forefathers, Hurry, let Your mercies go before us, For we have been very weak.
9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, saboda ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka kuma gafarta mana zunubanmu saboda sunanka.
Help us, O God of our salvation, Because of the glory of Your Name, And deliver us, and cover over our sins, For Your Name’s sake.
10 Don me al’ummai za su ce, “Ina Allahnsu yake?” A idanunmu, ka sanar wa al’ummai cewa kana ɗaukan fansar jinin bayinka da aka zubar.
Why do the nations say, “Where [is] their God?” Let [it] be known among the nations before our eyes, The vengeance of the blood of Your servants that is shed.
11 Bari nishe-nishen’yan kurkuku su zo gabanka; ta wurin ƙarfin hannunka ka kiyaye waɗanda aka yanke wa hukuncin mutuwa.
Let the groaning of the prisoner come in before You, According to the greatness of Your arm, Leave the sons of death.
12 Ka sāka a cinyoyin maƙwabtanmu sau bakwai zage-zagen da suka yi ta yi maka, ya Ubangiji.
And return to our neighbors, Sevenfold to their bosom, their reproach, With which they reproached You, O Lord.
13 Sa’an nan mu mutanenka, tumakin makiyayarka, za mu yabe ka har abada; daga tsara zuwa tsara za mu yi ta ba da labarin yabonka.
And we, Your people, and the flock of Your pasture, We give thanks to You for all time, We recount Your praise from generation to generation!

< Zabura 79 >