< Zabura 78 >
1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
AN INSTRUCTION OF ASAPH. Give ear, O my people, to my law, Incline your ear to sayings of my mouth.
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
I open my mouth with an allegory, I bring forth hidden things of old,
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
That we have heard and know, And our fathers have recounted to us.
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
We do not hide from their sons, Recounting praises of YHWH to a later generation, And His strength, and His wonders that He has done.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
And He raises up a testimony in Jacob, And has placed a law in Israel, That He commanded our fathers, To make them known to their sons.
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
So that a later generation knows, Sons who are born, rise and recount to their sons,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
And place their confidence in God, And do not forget the doings of God, But keep His commands.
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
And they are not like their fathers, A generation apostatizing and being rebellious, A generation—it has not prepared its heart, Nor [is] its spirit steadfast with God.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Sons of Ephraim—armed bearers of bow, Have turned in a day of conflict.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
They have not kept the covenant of God, And they have refused to walk in His law,
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
And they forget His doings, And His wonders that He showed them.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
He has done wonders before their fathers, In the land of Egypt—the field of Zoan.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
He cleft a sea, and causes them to pass over, Indeed, He causes waters to stand as a heap.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
And leads them with a cloud by day, And with a light of fire all the night.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
He cleaves rocks in a wilderness, And gives drink—as the great deep.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
And brings out streams from a rock, And causes waters to come down as rivers.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
And they still add to sin against Him, To provoke the Most High in the dry place.
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
And they try God in their heart, To ask food for their lust.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
And they speak against God—they said: “Is God able to array a table in a wilderness?”
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Behold, He has struck a rock, And waters flow, indeed, streams overflow. “Also, [is] He able to give bread? Does He prepare flesh for His people?”
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Therefore YHWH has heard, And He shows Himself angry, And fire has been kindled against Jacob, And anger has also gone up against Israel,
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
For they have not believed in God, Nor have they trusted in His salvation.
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
And He commands clouds from above, Indeed, He has opened doors of the heavens.
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
And He rains manna on them to eat, Indeed, He has given grain of the heavens to them.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Each has eaten food of the mighty, He sent provision to them to satiety.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
He causes an east wind to journey in the heavens, And leads a south wind by His strength,
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
And He rains on them flesh as dust, And as sand of the seas—winged bird,
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
And causes [it] to fall in the midst of His camp, Around His dwelling places.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
And they eat, and are greatly satisfied, And He brings their desire to them.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
They have not been estranged from their desire, Their food [is] yet in their mouth,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
And the anger of God has gone up against them, And He slays among their fat ones, And He caused youths of Israel to bend.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
With all this they have sinned again, And have not believed in His wonders.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
And He consumes their days in vanity, And their years in trouble.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
If He slew them, then they sought Him, And turned back, and earnestly sought God,
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
And they remember that God [is] their rock, And God Most High their redeemer.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
And they deceive Him with their mouth, And lie to Him with their tongue,
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
And their heart has not been right with Him, And they have not been steadfast in His covenant.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
And He, the Merciful One, pardons iniquity, and does not destroy, And has often turned back His anger, And does not awaken all His fury.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
And He remembers that they [are] flesh, A wind going on—and it does not return.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
How often do they provoke Him in the wilderness, Grieve Him in the desolate place?
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Indeed, they turn back, and try God, And have limited the Holy One of Israel.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
They have not remembered His hand The day He ransomed them from the adversary.
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
When He set His signs in Egypt, And His wonders in the field of Zoan,
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
And He turns their streams to blood, And they do not drink their floods.
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
He sends among them the beetle, and it consumes them, And the frog, and it destroys them,
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
And gives their increase to the caterpillar, And their labor to the locust.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
He destroys their vine with hail, And their sycamores with frost,
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
And delivers their beasts up to the hail, And their livestock to the burning flames.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
He sends on them the fury of His anger, Wrath, and indignation, and distress—A discharge of evil messengers.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
He ponders a path for His anger, He did not keep back their soul from death, Indeed, He delivered up their life to the pestilence.
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
And He strikes every firstborn in Egypt, The first-fruit of the strong in tents of Ham.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
And causes His people to journey as a flock, And guides them as a drove in a wilderness,
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
And He leads them confidently, And they have not been afraid, And the sea has covered their enemies.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
And He brings them to the border of His sanctuary, This mountain His right hand had acquired,
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
And casts out nations from before them, And causes them to fall in the line of inheritance, And causes the tribes of Israel to dwell in their tents,
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
And they tempt and provoke God Most High, And have not kept His testimonies.
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
And they turn back, And deal treacherously like their fathers, They have been turned like a deceitful bow,
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
And make Him angry with their high places, And make Him zealous with their carved images,
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
God has heard, and shows Himself angry. And kicks exceedingly against Israel.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
And He leaves the Dwelling Place of Shiloh, The tent He had placed among men,
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
And He gives His strength to captivity, And His beauty into the hand of an adversary,
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
And delivers His people up to the sword, And showed Himself angry with His inheritance.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Fire has consumed His young men, And His virgins have not been praised.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
His priests have fallen by the sword, And their widows do not weep.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
And the Lord wakes as a sleeper, As a mighty one crying aloud from wine.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
And He strikes His adversaries backward, He has put a continuous reproach on them,
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
And He kicks against the tent of Joseph, And has not fixed on the tribe of Ephraim.
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
And He chooses the tribe of Judah, With Mount Zion that He loved,
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
And builds His sanctuary as a high place, Like the earth, He founded it for all time.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
And He fixes on His servant David, And takes him from the folds of a flock,
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
He has brought him in from behind suckling ones, To rule over Jacob His people, And over Israel His inheritance.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
And he rules them according to the integrity of his heart, And leads them by the skillfulness of his hands!