< Zabura 79 >
1 Zabura ta Asaf. Ya Allah, al’ummai sun mamaye gādonka; sun ƙazantar da haikalinka mai tsarki, sun bar Urushalima kufai.
A Psalm of Asaph. O God, the Gentiles have entered into your inheritance; they have polluted your holy temple. They have set Jerusalem as a place to tend fruit trees.
2 Sun ba da gawawwakin bayinka kamar abinci ga tsuntsayen sararin sama, nama jikin tsarkakanka ga namun jejin duniya.
They have placed the dead bodies of your servants as food for the birds of the sky, the flesh of your saints for the beasts of the earth.
3 Sun zubar da jini kamar ruwa ko’ina a Urushalima, kuma babu wani da zai binne matattu.
They have poured out their blood like water all around Jerusalem, and there was no one who would bury them.
4 Mun zama abin reni ga maƙwabta, abin ba’a da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
We have become a disgrace to our neighbors, an object of ridicule and mockery to those who are around us.
5 Har yaushe, ya Ubangiji za ka yi ta fushi? Har abada ne? Har yaushe kishinka zai yi ta ƙuna kamar wuta?
How long, O Lord? Will you be angry until the end? Will your zeal be kindled like a fire?
6 Ka zuba fushinka a kan al’umman da ba su yarda da kai ba, a kan mulkokin da ba sa kira bisa sunanka;
Pour out your wrath among the Gentiles, who have not known you, and upon the kingdoms that have not invoked your name.
7 gama sun cinye Yaƙub suka lalatar da ƙasar zamansa.
For they have devoured Jacob, and they have desolated his place.
8 Kada ka riƙe zunubai kakanni a kanmu; bari jinƙanka yă zo da sauri yă sadu da mu, gama mun fid da zuciya sarai.
Do not remember our iniquities of the past. May your mercies quickly intercept us, for we have become exceedingly poor.
9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, saboda ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka kuma gafarta mana zunubanmu saboda sunanka.
Help us, O God, our Savior. And free us, Lord, for the glory of your name. And forgive us our sins for the sake of your name.
10 Don me al’ummai za su ce, “Ina Allahnsu yake?” A idanunmu, ka sanar wa al’ummai cewa kana ɗaukan fansar jinin bayinka da aka zubar.
Let them not say among the Gentiles, “Where is their God?” And may your name become known among the nations before our eyes. For the retribution of your servants’ blood, which has been poured out:
11 Bari nishe-nishen’yan kurkuku su zo gabanka; ta wurin ƙarfin hannunka ka kiyaye waɗanda aka yanke wa hukuncin mutuwa.
may the groans of the shackled enter before you. According to the greatness of your arm, take possession of the sons of those who have been killed.
12 Ka sāka a cinyoyin maƙwabtanmu sau bakwai zage-zagen da suka yi ta yi maka, ya Ubangiji.
And repay our neighbors sevenfold within their sinews. It is the reproach of the same ones who brought reproach against you, O Lord.
13 Sa’an nan mu mutanenka, tumakin makiyayarka, za mu yabe ka har abada; daga tsara zuwa tsara za mu yi ta ba da labarin yabonka.
But we are your people and the sheep of your pasture: we will give thanks to you in all ages. From generation to generation, we will announce your praise.