< Mahukunta 5 >
1 A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
In that day, Deborah and Barak, the son of Abinoam, sang out, saying:
2 “Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
“All you of Israel who have willingly offered your lives to danger, bless the Lord!
3 “Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Listen, O kings! Pay attention, O princes! It is I, it is I, who will sing to the Lord. I will sing a psalm to the Lord, the God of Israel!
4 “Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
O Lord, when you departed from Seir, and you crossed through the regions of Edom, the earth and the heavens were moved, and the clouds rained down water.
5 Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
The mountains flowed away before the face of the Lord, and Sinai, before the face of the Lord God of Israel.
6 “A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
In the days of Shamgar, the son of Anath, in the days of Jael, the paths were quiet. And whoever entered by them, walked along rough byways.
7 Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
The strong men ceased, and they rested in Israel, until Deborah rose up, until a mother rose up in Israel.
8 Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
The Lord chose new wars, and he himself overturned the gates of the enemies. A shield with a spear was not seen among the forty thousand of Israel.
9 Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
My heart loves the leaders of Israel. All you who, of your own free will, offered yourselves during a crisis, bless the Lord.
10 “Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
You who ride upon donkeys laboring, and you who sit in judgment, and you who walk along the way, speak out.
11 da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
Where the chariots were struck together, and the army of the enemies was choked, in that place, let the justices of the Lord be described, and let his clemency be for the brave of Israel. Then did the people of the Lord descend to the gates, and obtain leadership.
12 ‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
Rise up, rise up, O Deborah! Rise up, rise up, and speak a canticle! Rise up, Barak, and seize your captives, O son of Abinoam.
13 “Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
The remnants of the people were saved. The Lord contended with the strong.
14 Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
Out of Ephraim, he destroyed those with Amalek, and after him, out of Benjamin, those of your people, O Amalek. From Machir, there descended leaders, and from Zebulun, those who led the army to war.
15 ’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
The commanders of Issachar were with Deborah, and they followed the steps of Barak, who endangered himself, like one rushing headlong into a chasm. Reuben was divided against himself. Contention was found among great souls.
16 Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
Why do you live between two borders, so that you hear the bleating of the flocks? Reuben was divided against himself. Contention was found among great souls.
17 Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
Gilead rested beyond the Jordan, and Dan was occupied with ships. Asher was living on the shore of the sea, and dwelling in the ports.
18 Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
Yet truly, Zebulun and Naphtali offered their lives to death in the region of Merom.
19 “Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
The kings came and fought; the kings of Canaan fought at Taanach, beside the waters of Megiddo. And yet they took no spoils.
20 Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
The conflict against them was from heaven. The stars, remaining in their order and courses, fought against Sisera.
21 Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
The torrent of Kishon dragged away their carcasses, the onrushing torrent, the torrent of Kishon. O my soul, tread upon the stalwart!
22 Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
The hoofs of the horses were broken, while the strongest of the enemies fled away with fury, and rushed on to ruin.
23 Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
‘Cursed be the land of Meroz!’ said the Angel of the Lord. ‘Cursed be its inhabitants! For they did not come to the aid of the Lord, to the assistance of his most valiant men.’
24 “Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
Blessed among women is Jael, the wife of Heber the Kenite. And blessed is she in her tabernacle.
25 Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
He begged her for water, and she gave him milk, and she offered him butter in a dish fit for princes.
26 Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
She put her left hand to the nail, and her right hand to the workman’s mallet. And she struck Sisera, seeking in his head a place for the wound, and strongly piercing his temples.
27 A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
Between her feet, he was ruined. He fainted away and passed on. He curled up before her feet, and he lay there lifeless and miserable.
28 “Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
His mother gazed through a window and wailed. And she spoke from an upper room: ‘Why does his chariot delay in returning? Why are the feet of his team of horses so slow?’
29 Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
One who was wiser than the rest of his wives responded to her mother-in-law with this:
30 ‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
‘Perhaps he is now dividing the spoils, and the most beautiful among the women is being selected for him. Garments of diverse colors are being delivered to Sisera as spoils, and various goods are being collected for the adornment of necks.’
31 “Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.
O Lord, so may all your enemies perish! But may those who love you shine with splendor, as the sun shines at its rising.” And the land rested for forty years.