< Zabura 72 >

1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
Solomon’s. O God! thy justice, give, unto the king, And thy righteousness, unto the son of a king;
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
May he judge, Thy people with righteousness; And thine oppressed ones with justice;
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
May the mountains bring peace to the people, And the hills [be laden] with righteousness;
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
May he, Vindicate the oppressed of the people, Bring deliverance to the children of the needy, and, Crush the oppressor.
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
Let men revere thee, With the sun, And in presence of the moon, Unto the remotest generation.
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
Let him come down, Like rain on fields to be mown, Like myriad drops on land to be reaped.
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
May righteousness, in his days, blossom forth, And abundance of peace, till there be no moon.
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
So let him have dominion, From sea to sea, And from the River ["Euphrates"] unto the ends of the earth;
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
Before him, let the men of the desert kneel, But, as for his foes, the dust, let them lick;
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
The kings of Tarshish and of the Coastlands, A gift, let them render, The kings of Sheba and Seba, A present, let them bring;
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
Yea let all kings, bow down unto him, Let, all nations, serve him;
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
Because he Rescueth, The needy from the rich, The oppressed, who hath no helper;
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
He Pitieth the weak and the needy, And, the lives of the needy, he Saveth:
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
From extortion, and, violence, he Redeemeth their life, And precious is their blood in his sight.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
Let him live, then! And be there given unto him of the gold of Sheba, —Let prayer also be offered for him continually, All the day, let him be blessed.
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
May there be an abundance of corn in the earth, in the top of the mountains, —Let the fruit thereof, wave like Lebanon, And they of the city bloom like the fresh shoots of the earth.
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
May his Name be age-abiding, In the presence of the sun, let his Name flourish, —And may all the families of the ground bless themselves in him, All nations, pronounce him happy!
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
Blessed be Yahweh God, the God of Israel, —Who doeth wondrous things by himself alone;
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
And blessed be his glorious Name, unto times age-abiding, —And filled with his glory be all the earth, Amen and Amen!
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
Ended are the prayers of David, son of Jesse.

< Zabura 72 >