< Zabura 70 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
To the choirmaster of David to make remembrance. O God to deliver me O Yahweh to help my make haste!
2 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
May they be ashamed and they may be abashed [those who] seek life my may they be turned back backwards and may they be humiliated [the] [people] desirous of harm my.
3 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
May they turn back on [the] consequence of shame their those [who] say aha! - aha!
4 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Bari Allah yă sami ɗaukaka!”
May they exult and they may rejoice - in you all [those who] seek you and they may say continually may he be great God [those who] love salvation your.
5 Duk da haka ni matalauci ne da kuma mai bukata; ka zo da sauri gare ni, ya Allah. Kai ne mai taimakona da mai cetona; Ya Ubangiji, kada ka yi jinkiri.
And I - [am] poor and needy O God make haste! to me [are] help my and deliverer my you O Yahweh may not you delay.