< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
To the choirmaster a psalm of David. Hear O God voice my in complaint my from dread of an enemy you will preserve life my.
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
You will hide me from [the] secret counsel of evil-doers from [the] unrest of [those who] do wickedness.
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
Who they sharpen like sword tongue their they bend arrow their a word bitter.
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
To shoot in secret places [the] blameless suddenly they shoot at him and not they are afraid.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
They strengthen for themselves - a matter evil they speak to hide snares they say who? will he see them.
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
They plot injustice we have finished a plot plotted and [the] inner being of a person and [the] heart [is] deep.
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
And he shot at them God an arrow suddenly they will be wounds their.
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
And they caused to stumble him [is] on them tongue their they will shudder every [one who] looks on them.
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
And they were afraid all humankind and they declared [the] deed[s] of God and work his they will consider.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
Let him rejoice [the] righteous in Yahweh and he will take refuge in him and let them boast all [people] upright of heart.

< Zabura 64 >