< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
The psalm of David which he sung to the Lord for the words of Chusi the son of Jemini. O Lord my God, in thee have I put my trust: save me from all them that persecute me, and deliver me.
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
Lest at any time he seize upon my soul like a lion, while there is no one to redeem me, nor to save.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
O Lord my God, if I have done this thing, if there be iniquity in my hands:
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
If I have rendered to them that repaid me evils, let me deservedly fall empty before my enemies.
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
Let the enemy pursue my soul, and take it, and tread down my life on the earth, and bring down my glory to the dust.
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Rise up, O Lord, in thy anger: and be thou exalted in the borders of my enemies. And arise, O Lord my God, in the precept which thou hast commanded:
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
And a congregation of people shall surround thee. And for their sakes return thou on high.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
The Lord judgeth the people. Judge me, O Lord, according to my justice, and according to my innocence in me.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
The wickedness of sinners shall be brought to nought: and thou shalt direct the just: the searcher of hearts and reins is God.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
Just is my help from the Lord: who saveth the upright of heart.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
God is a just judge, strong and patient: is he angry every day?
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
Except you will be converted, he will brandish his sword: he hath bent his bow and made it ready.
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
And in it he hath prepared the instruments of death, he hath made ready his arrows for them that burn.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Behold he hath been in labour with injustice; he hath conceived sorrow, and brought forth iniquity.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
He hath opened a pit and dug it; and he is fallen into the hole he made.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
His sorrow shall be turned on his own head: and his iniquity shall comedown upon his crown.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I will give glory to the Lord according to his justice: and will sing to the name of the Lord the most high.

< Zabura 7 >