< Zabura 67 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Tare da kayan kiɗi masu tsirkiya. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă yi mana alheri yă kuma albarkace mu yă kuma sa fuskarsa ta haskaka a kanmu, (Sela)
Que Dios nos dé misericordia y bendición, y que la luz de su rostro brille sobre nosotros; (Selah)
2 don a san hanyoyinka a duniya, cetonka kuma a cikin dukan al’ummai.
Para que los hombres vean tu camino en la tierra, y tu salvación entre todas las naciones.
3 Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe ka.
Que los pueblos te den alabanza, oh Dios; deja que todos los pueblos te den elogios.
4 Bari al’ummai su yi murna su kuma rera don farin ciki, gama kana mulkin mutanenka da adalci kana kuma bi da al’umman duniya. (Sela)
Que las naciones se regocijen, y hablen de gozo; porque tú serás el juez de los pueblos en justicia, que guiarás a las naciones de la tierra. (Selah)
5 Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe.
Deja que los pueblos te den alabanza, oh Dios; deja que todos los pueblos te den elogios.
6 Sa’an nan ƙasa za tă ba da girbinta Allah kuma, Allahnmu, zai albarkace mu.
La tierra le dio aumento; y Dios, nuestro Dios, nos dará su bendición.
7 Allah yă sa mana albarka, dukan iyakar duniya kuma su ji tsoronsa.
Dios nos dará su bendición; así que todos los confines de la tierra le teman.

< Zabura 67 >