< Zabura 67 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Tare da kayan kiɗi masu tsirkiya. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă yi mana alheri yă kuma albarkace mu yă kuma sa fuskarsa ta haskaka a kanmu, (Sela)
Nkulunkulu, woba lomusa kithi usibusise, ukhanyise ubuso bakho phezu kwethu. (Sela)
2 don a san hanyoyinka a duniya, cetonka kuma a cikin dukan al’ummai.
Ukuze indlela yakho yaziwe emhlabeni, usindiso lwakho ezizweni zonke.
3 Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe ka.
Kazikudumise izizwe, Nkulunkulu, kabakudumise abantu bonke.
4 Bari al’ummai su yi murna su kuma rera don farin ciki, gama kana mulkin mutanenka da adalci kana kuma bi da al’umman duniya. (Sela)
Izizwe kazijabule zihlabele ngentokozo, ngoba uzabahlulela abantu ngokuqonda, uhole izizwe emhlabeni. (Sela)
5 Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe.
Kazikudumise izizwe, Nkulunkulu, kabakudumise abantu bonke.
6 Sa’an nan ƙasa za tă ba da girbinta Allah kuma, Allahnmu, zai albarkace mu.
Umhlaba uzathela izithelo zawo; uNkulunkulu, uNkulunkulu wethu uzasibusisa.
7 Allah yă sa mana albarka, dukan iyakar duniya kuma su ji tsoronsa.
UNkulunkulu uzasibusisa, layo yonke imikhawulo yomhlaba izamesaba.

< Zabura 67 >