< Zabura 66 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
Til sangmesteren; en sang, en salme. Rop med fryd for Gud, all jorden!
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Syng ut hans navns ære, gi ham ære til hans pris!
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Si til Gud: Hvor forferdelige er dine gjerninger! For din store makts skyld skal dine fiender hykle for dig.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
All jorden skal tilbede dig og lovsynge dig, de skal lovsynge ditt navn. (Sela)
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Kom og se Guds gjerninger! Han er forferdelig i gjerning mot menneskenes barn.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Han gjorde havet om til tørt land, gjennem strømmen gikk de til fots; der gledet vi oss i ham.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
Han hersker med sitt velde evindelig, hans øine gir akt på hedningene; de gjenstridige må ikke ophøie sig. (Sela)
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
I folkeslag, lov vår Gud og forkynn hans pris med høi røst,
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
han som holdt vår sjel i live og ikke lot vår fot vakle!
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
For du prøvde oss, Gud, du renset oss, likesom de renser sølv.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Du førte oss inn i et garn, du la en trykkende byrde på våre lender.
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Du lot mennesker fare frem over vårt hode; vi kom i ild og i vann. Men du førte oss ut til vederkvegelse.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
Jeg vil gå inn i ditt hus med brennoffer, jeg vil gi dig det jeg har lovt,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
det som gikk over mine leber, og som min munn talte i min nød.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
Jeg vil ofre dig brennoffere av fett kveg med duft av værer; jeg vil ofre okser tillikemed bukker. (Sela)
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Kom, hør, alle I som frykter Gud; jeg vil fortelle hvad han har gjort mot min sjel.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
Til ham ropte jeg med min munn, og lovsang var under min tunge.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Hadde jeg urett for øie i mitt hjerte, så vilde Herren ikke høre.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
Men Gud har hørt, han har aktet på mitt bønnerop.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Lovet være Gud, som ikke avviste min bønn og ikke tok sin miskunnhet fra mig!

< Zabura 66 >