< Zabura 65 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Wata waƙa. Yabo ya dace da kai, ya Allah, a Sihiyona; a gare ka za mu cika alkawuranmu
Til sangmesteren; en salme av David; en sang. Dig, Gud, priser de i stillhet på Sion, og dig gir de det de har lovt.
2 Ya kai wanda yake jin addu’a a gare ka dukan mutane za su zo.
Du som hører bønner, til dig kommer alt kjød.
3 Sa’ad da zunubai suka sha ƙarfinmu, ka gafarta laifofinmu.
Når mine misgjerninger er blitt mig for svære, så forlater du våre overtredelser.
4 Masu albarka ne waɗanda ka zaɓa ka kawo kusa don su zauna a filayenka! Mun cika da abubuwa masu kyau na gidanka, na haikalinka mai tsarki.
Salig er den du utvelger og lar komme nær, så han bor i dine forgårder; vi vil mette oss med de gode ting i ditt hus, ditt hellige tempel.
5 Ka amsa mana da ayyuka masu banmamaki na adalci, Ya Allah Mai Cetonmu, begen dukan iyakar duniya da kuma na tekuna masu nesa,
Med forferdelige gjerninger bønnhører du oss i rettferdighet, du vår frelses Gud, du som er en tilflukt for alle jordens ender og havet langt borte.
6 wanda ya yi duwatsu ta wurin ikonka, bayan ka kintsa kanka da ƙarfi,
Han gjør fjellene faste med sin kraft, omgjordet med velde.
7 wanda ya kwantar da rurin tekuna, rurin raƙumansu, da kuma tumbatsar al’ummai.
Han stiller havenes brusen, deres bølgers brusen og folkenes bulder.
8 Waɗanda suke zama can da nesa sukan ji tsoron manyan ayyukanka; inda safe ke haskaka yamma kuma ta shuɗe kakan sa a yi waƙoƙin farin ciki.
Og de som bor ved jordens ender, frykter for dine tegn; de steder hvor morgen og aften bryter frem, fyller du med jubel.
9 Kana kula da ƙasa kana kuma yi mata banruwa; kana azurta ta a yalwace. Rafuffukan Allah sun cika da ruwa don su ba mutane hatsi, don haka ne ka ƙaddara.
Du har gjestet jorden og gitt den overflod, gjort den såre rik, Guds bekk er full av vann; du har latt dem få sitt korn, for således lager du jorden til.
10 Ka kwarara ta da ruwa ka kuma baje kunyoyinta; ka sa ta yi laushi da yayyafi ka kuma albarkaci tsire-tsirenta.
Du vannet dens furer, senket dens plogland; du bløtte den med regnskurer, velsignet dens grøde.
11 Saboda alherinka, ya Allah, an sami kaka mai albarka, amalankenka kuwa sun cika har suna zuba.
Du har kronet din godhets år, og dine fotspor drypper av fedme.
12 Makiyayan hamada sun cika har suna zuba; tuddai sun rufu da murna.
Ødemarkens beiter drypper, og haugene omgjorder sig med jubel.
13 Wurin dausayin kiwo sun rufu da garkuna kwari kuma sun cika da hatsi; suna sowa don farin ciki.
Engene er klædd med får, og dalene er dekket med korn; folk roper med fryd og synger.

< Zabura 65 >