< Zabura 66 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
Psalmus In finem, Canticum Psalmi resurrectionis. Iubilate Deo omnis terra,
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
psalmum dicite nomini eius: date gloriam laudi eius.
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Dicite Deo quam terribilia sunt opera tua Domine! in multitudine virtutis tuae mentientur tibi inimici tui.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
Omnis terra adoret te, et psallat tibi: psalmum dicat nomini tuo.
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Venite, et videte opera Dei: terribilis in consiliis super filios hominum.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Qui convertit mare in aridam, in flumine pertransibunt pede: ibi laetabimur in ipso.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
Qui dominatur in virtute sua in aeternum, oculi eius super gentes respiciunt: qui exasperant non exaltentur in semetipsis.
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Benedicite Gentes Deum nostrum: et auditam facite vocem laudis eius,
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
Qui posuit animam meam ad vitam: et non dedit in commotionem pedes meos.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
Quoniam probasti nos Deus: igne nos examinasti, sicut examinatur argentum.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Induxisti nos in laqueum, posuisti tribulationes in dorso nostro:
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
imposuisti homines super capita nostra. Transivimus per ignem et aquam: et eduxisti nos in refrigerium.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
Introibo in domum tuam in holocaustis: reddam tibi vota mea,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
quae distinxerunt labia mea. Et locutum est os meum, in tribulatione mea.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
Holocausta medullata offeram tibi cum incenso arietum: offeram tibi boves cum hircis.
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Venite, audite, et narrabo, omnes qui timetis Deum, quanta fecit animae meae.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
Ad ipsum ore meo clamavi, et exultavi sub lingua mea.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Iniquitatem si aspexi in corde meo, non exaudiet Dominus.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
Propterea exaudivit Deus, et attendit voci deprecationis meae.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Benedictus Deus, qui non amovit orationem meam, et misericordiam suam a me.

< Zabura 66 >