< Zabura 6 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Přednímu kantoru na neginot, k nízkému zpěvu, žalm Davidův. Hospodine, netresci mne v hněvě svém, ani v prchlivosti své kárej mne.
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
Smiluj se nade mnou, Hospodine, neboť jsem zemdlený; uzdrav mne, Hospodine, nebo ztrnuly kosti mé.
3 Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
Ano i duše má předěšena jest náramně, ty pak, Hospodine, až dokavad?
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
Navratiž se, Hospodine, a vytrhni duši mou; spomoz mi pro milosrdenství své.
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol h7585)
Nebo mrtví nezpomínají na tebe, a v hrobě kdo tě bude oslavovati? (Sheol h7585)
6 Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
Ustávám v úpění svém, ložce své každé noci svlažuji, slzami svými postel svou smáčím.
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
Sškvrkla se zámutkem tvář má, sstarala se příčinou všech nepřátel mých.
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
Odstuptež ode mne všickni činitelé nepravosti; neboť jest vyslyšel Hospodin hlas pláče mého.
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
Vyslyšel Hospodin pokornou modlitbu mou, Hospodin modlitbu mou přijal.
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.
Nechažť se zastydí a předěsí zřejmě všickni nepřátelé moji, nechažť jsou zpět obráceni a rychle zahanbeni.

< Zabura 6 >