< Zabura 5 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Busa. Ta Dawuda. Ka saurare kalmomina, ya Ubangiji, ka ji ajiyar zuciyata.
Přednímu zpěváku na nechilot, žalm Davidův. Slova má slyš, Hospodine, porozuměj tužebnému úpění mému.
2 Ka saurare kukata na neman taimako, Sarkina da Allahna, gama gare ka nake addu’a.
Pozoruj hlasu volání mého, králi můj a Bože můj; nebo se tobě modlím.
3 Da safe, ya Ubangiji, ka ji muryata; da safe na gabatar da bukatuna a gabanka in kuma jira da sa zuciya.
Hospodine, v jitře vyslyšíš hlas můj, v jitře předložím tobě žádost, a šetřiti budu.
4 Kai ba Allahn da yake jin daɗin mugu ba ne; gama kana gāba da dukan masu aikata mugunta.
Nebo ty, ó Bože silný, neoblibuješ bezbožnosti, nemá místa u tebe nešlechetník.
5 Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.
Neostojí blázniví před očima tvýma, v nenávisti máš všecky činitele nepravosti.
6 Kakan hallaka masu yin ƙarya. Masu kisankai da mutane masu ruɗu Ubangiji yana ƙyama.
Zatratíš mluvící lež. Èlověka ukrutného a lstivého v ohavnosti má Hospodin.
7 Amma ni, ta wurin jinƙanka mai girma, zan shiga gidanka; da bangirma zan durƙusa ga haikalinka.
Já pak ve množství milosrdenství tvého vejdu do domu tvého, klaněti se budu k svatému chrámu tvému v bázni tvé.
8 Ka bi da ni, ya Ubangiji, cikin adalcinka saboda abokan gābana, ka fayyace hanyarka a gabana.
Hospodine, proveď mne v spravedlnosti své, pro ty, jenž mne střehou; spravuj přede mnou cestu svou.
9 Babu ko kalma guda daga bakinsu da za a dogara da ita; marmarinsu kawai shi ne su hallakar da waɗansu. Maƙogwaronsu buɗaɗɗen kabari ne; da harshensu suna faɗin ƙarya.
Neboť není v ústech jejich žádné upřímnosti, vnitřnosti jejich plné nešlechetnosti, hrob otevřený hrdlo jejich, jazykem svým lahodně mluví.
10 Ka furta su masu laifi, ya Allah! Bari makircinsu yă zama fāɗuwarsu. Ka kore su saboda yawan zunubansu, saboda sun tayar maka.
Zkaz je, ó Bože, nechať padnou od rad svých; pro množství nešlechetností jejich rozptyl je, poněvadž odporní jsou tobě.
11 Amma bari dukan waɗanda suke neman mafaka gare ka su yi murna; bari kullum su yi ta rerawa saboda farin ciki. Ka buɗe kāriyarka a bisansu, domin waɗanda suke ƙaunar sunanka su yi farin ciki a cikinka.
A ať se všickni v tě doufající radují, na věky ať plésají, když je zastírati budeš; ať se v tobě veselí, kteřížkoli milují jméno tvé.
12 Gama tabbatacce, ya Ubangiji, kakan albarkaci adalai; kakan kewaye su da tagomashinka kamar garkuwa.
Nebo ty, Hospodine, požehnáš spravedlivému, a jako štítem přívětivostí svou vůkol zastřeš jej.

< Zabura 5 >