< Zabura 5 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Busa. Ta Dawuda. Ka saurare kalmomina, ya Ubangiji, ka ji ajiyar zuciyata.
Give ear to my words, O Jehovah, Consider my (meditation)
2 Ka saurare kukata na neman taimako, Sarkina da Allahna, gama gare ka nake addu’a.
Hearken to the voice of my cry, my King, and my God, for to thee do I pray.
3 Da safe, ya Ubangiji, ka ji muryata; da safe na gabatar da bukatuna a gabanka in kuma jira da sa zuciya.
O Jehovah, in the morning thou shall hear my voice. In the morning I will direct to thee, and will keep watch.
4 Kai ba Allahn da yake jin daɗin mugu ba ne; gama kana gāba da dukan masu aikata mugunta.
For thou are not a God who has pleasure in wickedness. Evil shall not sojourn with thee.
5 Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.
The arrogant shall not stand in thy sight. Thou hate all workers of iniquity.
6 Kakan hallaka masu yin ƙarya. Masu kisankai da mutane masu ruɗu Ubangiji yana ƙyama.
Thou will destroy those who speak lies. Jehovah abhors the blood-thirsty and deceitful man.
7 Amma ni, ta wurin jinƙanka mai girma, zan shiga gidanka; da bangirma zan durƙusa ga haikalinka.
But as for me, in the abundance of thy loving kindness I will come into thy house. In thy fear I will worship toward thy holy temple.
8 Ka bi da ni, ya Ubangiji, cikin adalcinka saboda abokan gābana, ka fayyace hanyarka a gabana.
Lead me, O Jehovah, in thy righteousness because of my enemies. Make thy way straight before my face.
9 Babu ko kalma guda daga bakinsu da za a dogara da ita; marmarinsu kawai shi ne su hallakar da waɗansu. Maƙogwaronsu buɗaɗɗen kabari ne; da harshensu suna faɗin ƙarya.
For there is no faithfulness in their mouth. Their inward part is very wickedness. Their throat is an open sepulcher. With their tongue they deceive.
10 Ka furta su masu laifi, ya Allah! Bari makircinsu yă zama fāɗuwarsu. Ka kore su saboda yawan zunubansu, saboda sun tayar maka.
Hold them guilty, O God. Let them fall by their own counsels. Thrust them out in the multitude of their transgressions. For they have rebelled against thee.
11 Amma bari dukan waɗanda suke neman mafaka gare ka su yi murna; bari kullum su yi ta rerawa saboda farin ciki. Ka buɗe kāriyarka a bisansu, domin waɗanda suke ƙaunar sunanka su yi farin ciki a cikinka.
But let all those who take refuge in thee rejoice. Let them ever shout for joy, because thou defend them. Let those also who love thy name be joyful in thee.
12 Gama tabbatacce, ya Ubangiji, kakan albarkaci adalai; kakan kewaye su da tagomashinka kamar garkuwa.
For thou will bless the righteous man, O Jehovah. Thou will encompass him with favor as with a shield. (Selah)

< Zabura 5 >