< Zabura 4 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
Answer me when I call, O God of my righteousness. Thou have enlarged me in distress. Have mercy upon me, and hear my prayer.
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
O ye sons of men, how long shall my glory be turned into dishonor? Will ye love vanity, and seek after falsehood? (Selah)
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
But know that Jehovah has set apart for himself him who is holy. Jehovah will hear when I call to him.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Stand in awe, and sin not. Commune with your own heart upon your bed, and be still. (Selah)
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Offer the sacrifices of righteousness, and put your trust in Jehovah.
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Many there are who say, Who will show us good? Jehovah, lift thou up the light of thy countenance upon us.
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
Thou have put gladness in my heart more than when their grain and their new wine are increased.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
In peace I will both lie down and sleep, for thou, Jehovah, alone make me dwell in safety.