< Zabura 49 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
För sångmästaren; av Koras söner; en psalm. Hören detta, alla folk, lyssnen härtill, I alla som leven i världen,
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
både låga och höga, rika såväl som fattiga.
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
Hin mun skall tala visdom, och mitt hjärtas tanke skall vara förstånd.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
Jag vill böja mitt öra till lärorikt tal, jag vill yppa vid harpan min förborgade kunskap.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Varför skulle jag frukta i olyckans dagar, när mina förföljares ondska omgiver mig?
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
De förlita sig på sina ägodelar och berömma sig av sin stora rikedom.
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
Men sin broder kan ingen förlossa eller giva Gud lösepenning för honom.
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
För dyr är lösen för hans själ och kan icke betalas till evig tid,
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
så att han skulle få leva för alltid och undgå att se graven.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
Nej, man skall se att visa män dö, att dårar och oförnuftiga förgås likasom de; de måste lämna sina ägodelar åt andra.
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
De tänka att deras hus skola bestå evinnerligen, deras boningar från släkte till släkte; de uppkalla jordagods efter sina namn.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Men en människa har, mitt i sin härlighet, intet bestånd, hon är lik fänaden, som förgöres.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
Den vägen gå de, dårar som de äro, och de följas av andra som finna behag i deras tal. (Sela)
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol )
Såsom en fårhjord drivas de ned till dödsriket, där döden bliver deras herde. Så få de redliga makt över dem, när morgonen gryr, medan deras skepnader förtäras av dödsriket och ej få annan boning. (Sheol )
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol )
Men min själ skall Gud förlossa ifrån dödsrikets våld, ty han skall upptaga mig. (Sela) (Sheol )
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Frukta icke, när en man bliver rik, när hans hus växer till i härlighet.
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
Ty av allt detta får han vid sin död intet med sig, och hans härlighet följer honom icke ditned.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Om han ock prisar sig välsignad under sitt liv, ja, om man än berömmer dig, när du gör goda dagar,
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
så skall dock vars och ens själ gå till hans fäders släkte, till dem som aldrig mer se ljuset.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
En människa som, mitt i sin härlighet, är utan förstånd, hon är lik fänaden, som förgöres.