< Zabura 48 >

1 Waƙa ce. Zabura ta’ya’yan Kora maza. Ubangiji mai girma ne, kuma mafificin yabo, a birnin Allahnmu, dutsensa mai tsarki.
A Canticle Psalm. To the sons of Korah, on the second Sabbath. The Lord is great and exceedingly praiseworthy, in the city of our God, on his holy mountain.
2 Kyakkyawa ce cikin tsayinta, abin farin cikin dukan duniya. Kamar ƙwanƙoli mafi tsayi na Zafon ne Dutsen Sihiyona, birnin Babban Sarki.
Mount Zion is being founded with the exultation of the whole earth, on the north side, the city of the great king.
3 Allah yana cikin fadodinta; ya nuna kansa mafaka ce gare ta.
In her houses, God will be known, since he will support her.
4 Sa’ad da sarakuna suka haɗa rundunoni, sa’ad da suka yi gaba tare,
For behold, the kings of the earth have been gathered together; they have convened as one.
5 sun gan ta suka kuwa yi mamaki; suka gudu don tsoro.
Such did they see, and they were astonished: they were disturbed, they were moved.
6 Rawar jiki ya kama su a can, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Trembling took hold of them. In that place, their pains were that of a woman in labor.
7 Ka hallaka su kamar jiragen ruwan Tarshish da iskar gabas ta wargaje.
With a vehement spirit, you will crush the ships of Tarshish.
8 Yadda muka ji, haka muka gani a cikin birnin Ubangiji Maɗaukaki, a cikin birnin Allahnmu. Allah ya sa ta zauna lafiya har abada. (Sela)
As we have heard, so we have seen, in the city of the Lord of hosts, in the city of our God. God has founded it in eternity.
9 Cikin haikalinka, ya Allah, mun yi tunani a kan ƙaunarka marar ƙarewa.
We have received your mercy, O God, in the midst of your temple.
10 Kamar sunanka, ya Allah, yabonka ya kai iyakokin duniya; hannunka na dama ya cika da adalci.
According to your name, O God, so does your praise reach to the ends of the earth. Your right hand is full of justice.
11 Dutsen Sihiyona ya yi farin ciki, ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukuntanka.
Let mount Zion rejoice, and let the daughters of Judah exult, because of your judgments, O Lord.
12 Yi tafiya cikin Sihiyona, ku kewaye ta, ku ƙirga hasumiyoyinta,
Encircle Zion and embrace her. Discourse in her towers.
13 ku lura da katangarta da kyau, ku dubi fadodinta, don ku faɗe su ga tsara mai zuwa.
Set your hearts on her virtue. And distribute her houses, so that you may discourse of it in another generation.
14 Gama wannan Allah shi ne Allahnmu har abada abadin; zai zama jagorarmu har zuwa ƙarshe.
For this is God, our God, in eternity and forever and ever. He will rule us forever.

< Zabura 48 >