< Zabura 47 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
Сви народи, запљескајте рукама, покликните Богу гласом радосним.
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
Јер је Вишњи Господ страшан, цар велики над свом земљом.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
Покори нам народе и племена под ноге наше.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
Избра нам достојање наше, красоту Јакова, који Му омиле.
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
Иде Бог уз подвикивање, Господ уз глас трубни.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Појте Богу, појте; појте цару нашем, појте;
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
Јер је Бог цар од све земље, појте песму.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
Бог царује над народима; Бог седи на светом престолу свом.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Кнезови народни састављају се с народом Бога Аврамовог. Јер су штитови земаљски Божији. Да је узвишен!