< Karin Magana 1 >
1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
Приче Соломуна сина Давидовог, цара Израиљевог,
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
Да се познаје мудрост и настава, да се разумеју речи разумне,
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
Да се прима настава у разуму, у правди, у суду и у свему што је право,
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
Да се даје лудима разборитост, младићима знање и помњивост.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Мудар ће слушати и више ће знати, и разуман ће стећи мудрост,
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
Да разуме приче и значење, речи мудрих људи и загонетке њихове.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
Почетак је мудрости страх Господњи; луди презиру мудрост и наставу.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Слушај, сине, наставу оца свог, и не остављај науке матере своје.
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
Јер ће бити венац од милина око главе твоје, и гривна на грлу твом.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Сине мој, ако би те мамили грешници, не пристај;
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
Ако би рекли: Ходи с нама да вребамо крв, да заседамо правоме низашта;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol )
Прождрећемо их као гроб живе, и свеколике као оне који силазе у јаму; (Sheol )
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
Свакојаког блага добићемо, напунићемо куће своје плена;
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Бацаћеш жреб свој с нама; један ће нам тоболац бити свима;
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
Сине мој, не иди на пут с њима, чувај ногу своју од стазе њихове.
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
Јер ногама својим трче на зло и хите да проливају крв.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Јер се узалуд разапиње мрежа на очи свакој птици;
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
А они вребају своју крв и заседају својој души.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Такви су путеви свих лакомих на добитак, који узима душу својим господарима.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
Премудрост виче на пољу, на улицама пушта глас свој;
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
У највећој вреви виче, на вратима, у граду говори своје беседе;
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
Луди, докле ћете љубити лудост? И подсмевачима докле ће бити мио подсмех? И безумни, докле ће мрзети на знање?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Обратите се на карање моје; ево, изасућу вам дух свој, казаћу вам речи своје.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Што звах, али не хтесте, пружах руку своју, али нико не мари,
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
Него одбацисте сваки савет мој, и карање моје не хтесте примити;
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
Зато ћу се и ја смејати вашој невољи, ругаћу се кад дође чега се бојите;
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
Кад као пустош дође чега се бојите, и погибао ваша као олуја кад дође, кад навали на вас невоља и мука.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Тада ће ме звати, али се нећу одазвати; рано ће тражити, али ме неће наћи.
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Јер мрзише на знање, и страх Господњи не изабраше;
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
Не присташе на мој савет, и презираше сва карања моја.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Зато ће јести плод од путева својих, и наситиће се савета својих.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Јер ће луде убити мир њихов, и безумне ће погубити срећа њихова.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Али ко ме слуша боравиће безбрижно, и биће на миру не бојећи се зла.