< Zabura 46 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
ʼElohim es nuestro Refugio y Fortaleza, Un auxilio muy presente en la tribulación.
2 Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
Por tanto, no temeremos aunque la tierra sea removida, Y las montañas se traspasen al corazón del mar,
3 ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
Aunque bramen y espumen sus aguas, Y tiemblen las montañas a causa de su ímpetu. (Selah)
4 Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
Hay un río cuyas corrientes alegran la ciudad de ʼElohim, El Santuario, morada del ʼElyón.
5 Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
ʼElohim está en medio de ella. No será conmovida. ʼElohim la ayudará al clarear la mañana.
6 Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
Braman las naciones, Se tambalean los reinos. Él emite su voz. Se derrite la tierra.
7 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
Yavé de las huestes está con nosotros. Nuestro Refugio es el ʼElohim de Jacob. (Selah)
8 Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
Vengan y miren las obras de Yavé, Quien causó asolamientos en la tierra,
9 Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
Quien hace cesar las guerras hasta el fin de la tierra, Quien quiebra el arco, rompe la lanza Y quema los carruajes en el fuego.
10 “Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
Estén quietos y reconozcan que Yo soy ʼElohim. Seré exaltado entre las naciones. Seré enaltecido en la tierra.
11 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
Yavé de las huestes está con nosotros. Nuestra Fortaleza es el ʼElohim de Jacob. (Selah)