< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Den gracias a Yavé, porque Él es bueno, Porque para siempre es su misericordia.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Diga ahora Israel: Que para siempre es su misericordia.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Diga la casa de Aarón: Que para siempre es su misericordia.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Digan ahora los que temen a Yavé: Que para siempre es su misericordia.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
En mi angustia clamé a YA, Y YA me respondió Y me colocó en lugar amplio.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Yavé está conmigo, No temeré Lo que me haga el hombre.
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Yavé está conmigo entre los que me ayudan. Por tanto veré mi deseo en los que me odian.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Mejor es refugiarse en Yavé Que confiar en hombre.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Mejor es refugiarse en Yavé Que confiar en los poderosos.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Todas las naciones me rodearon. En el Nombre de Yavé yo las destruiré.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Me rodearon, Sí, me asediaron. En el Nombre de Yavé ciertamente las destruiré.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Me rodearon como abejas. Se extinguieron como fuego de espinos. En el Nombre de Yavé yo ciertamente las destruiré.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Ustedes me empujaron con violencia De modo que estaba cayendo, Pero me ayudó Yavé.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Mi Fortaleza y mi Canto es YA. Él es mi salvación.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Voz de júbilo y de salvación hay en las tiendas de los justos. La mano derecha de Yavé hace proezas.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
La mano derecha de Yavé está levantada en alto. La mano derecha de Yavé realiza hazañas.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
No moriré, sino viviré, Y contaré las obras de YA.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Me disciplinó severamente YA, Pero no me entregó a la muerte.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Ábranme las puertas de la justicia. Entraré por ellas, Daré gracias a YA.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Esta es la puerta de Yavé. Por ella entrarán los justos.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Te alabaré porque me escuchaste, Y fuiste mi salvación.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
La piedra que desecharon los edificadores Es cabeza del ángulo.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
Esta es la obra de Yavé. Es maravillosa ante nuestros ojos.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Este es el día que hizo Yavé. ¡Regocijémonos y alegrémonos en él!
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Te imploramos, oh Yavé. ¡Sálvanos ahora! Te rogamos, oh Yavé que nos prosperes ahora.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
¡Bendito el que viene en el Nombre de Yavé! Desde la Casa de Yavé los bendecimos.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
ʼEL es Yavé, y nos dio luz, Aten con cuerdas sacrificios festivos a los cuernos del altar.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Tú eres mi ʼEL, y te doy gracias. Tú eres mi ʼElohim, te exaltaré.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Den gracias a Yavé porque Él es bueno, Porque para siempre es su misericordia.

< Zabura 118 >