< Zabura 41 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
For the choirmaster. A Psalm of David. Blessed is the one who cares for the poor; the LORD will deliver him in the day of trouble.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
The LORD will protect and preserve him; He will bless him in the land and refuse to surrender him to the will of his foes.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
The LORD will sustain him on his bed of illness and restore him from his bed of sickness.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
I said, “O LORD, be gracious to me; heal me, for I have sinned against You.”
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
My enemies say with malice: “When will he die and be forgotten?”
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
My visitor speaks falsehood; he gathers slander in his heart; he goes out and spreads it abroad.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
All who hate me whisper against me; they imagine the worst for me:
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
“A vile disease has been poured into him; he will never get up from where he lies!”
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Even my close friend whom I trusted, the one who shared my bread, has lifted up his heel against me.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
But You, O LORD, be gracious to me and raise me up, that I may repay them.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
By this I know that You delight in me, for my enemy does not triumph over me.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
In my integrity You uphold me and set me in Your presence forever.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Blessed be the LORD, the God of Israel, from everlasting to everlasting. Amen and Amen.

< Zabura 41 >