< Zabura 4 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
in finem in carminibus psalmus David cum invocarem exaudivit me Deus iustitiae meae in tribulatione dilatasti mihi miserere mei et exaudi orationem meam filii hominum usquequo gravi corde ut quid diligitis vanitatem et quaeritis mendacium diapsalma
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
et scitote quoniam mirificavit Dominus sanctum suum Dominus exaudiet me cum clamavero ad eum
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
irascimini et nolite peccare quae dicitis in cordibus vestris in cubilibus vestris conpungimini diapsalma
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
sacrificate sacrificium iustitiae et sperate in Domino multi dicunt quis ostendet nobis bona
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
signatum est super nos lumen vultus tui Domine dedisti laetitiam in corde meo
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
a fructu frumenti et vini et olei sui multiplicati sunt
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
in pace in id ipsum dormiam et requiescam
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
quoniam tu Domine singulariter in spe constituisti me