< Zabura 3 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
psalmus David cum fugeret a facie Abessalon filii sui Domine quid multiplicati sunt qui tribulant me multi insurgunt adversum me
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
multi dicunt animae meae non est salus ipsi in Deo eius diapsalma
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
tu autem Domine susceptor meus es gloria mea et exaltans caput meum
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
voce mea ad Dominum clamavi et exaudivit me de monte sancto suo diapsalma
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
ego dormivi et soporatus sum exsurrexi quia Dominus suscipiet me
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
non timebo milia populi circumdantis me exsurge Domine salvum me fac Deus meus
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
quoniam tu percussisti omnes adversantes mihi sine causa dentes peccatorum contrivisti
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
Domini est salus et super populum tuum benedictio tua

< Zabura 3 >