< Zabura 4 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
For the music director. A psalm of David, to be accompanied by string instruments. When I call, please answer me, God who vindicates me. When I was hemmed in by troubles, you gave me a way out. Be gracious to me and hear my prayer.
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
How long will you people ruin my reputation? How long will you love what is worthless and tell lies? (Selah)
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
You should realize that the Lord shows special favor to the faithful. The Lord listens when I call to him.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Be in awe, do not sin. When you rest, reflect on this, and keep quiet! (Selah)
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Offer sacrifices with the right attitude. Trust in the Lord.
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Many say, “Who is going to show us some good?” Lord, may your face shine upon us.
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
The happiness you give me is better than those who have a plentiful harvest of grain and new wine.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
I will lie down in peace and sleep, for you, Lord, alone keep me safe.

< Zabura 4 >