< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
A psalm of David. Honor the Lord, children of God, honor his glory and strength.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Honor the Lord for his glorious character, bow in reverence to the Lord in his brilliant holiness.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
The Lord's voice sounds over the sea. The God of glory thunders. The Lord thunders over the vast ocean.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
The Lord's voice is powerful; the Lord's voice is majestic;
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
the Lord's voice shatters the cedars, even breaking the cedars of Lebanon.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
He makes the mountains of Lebanon skip like a calf, and Mount Hermon like a young wild ox.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
The Lord's voice blazes out like lightning flashes.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
The Lord's voice causes an earthquake in the desert; the desert of Kadesh shakes.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
The Lord's voice makes the pregnant deer go into labor; it strips bare the forests. In his Temple all the worshipers shout, “Glory!”
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
The Lord sits on his throne above the floodwaters; the Lord is the eternal King.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
The Lord gives strength to his people; the Lord blesses them with peace.

< Zabura 29 >