< Zabura 36 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
Для дириґента хору. Раба Господнього Давида. Грішне слово безбожного в серці моїм: „Нема страху́ Божого перед очима його“,
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
бо в очах своїх він до себе підлещується, щоб бу́цім то гріх свій знайти, щоб знена́видіти.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
Слова́ його уст — то марно́та й обма́на, перестав він бути мудрим, щоб чинити добро́.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
Беззако́нство заду́мує він на посте́лі своїй, стає на дорозі недобрій, не цурається злого.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
Господи, — аж до небе́с милосердя Твоє, аж до хмар Твоя вірність,
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
Твоя справедливість — немов гори Божі, Твої суди — безо́дня велика, люди́ну й худо́бу спасаєш Ти, Господи!
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
Яка дорога́ Твоя милість, о Боже, і ховаються лю́дські сини в тіні́ Твоїх крил:
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
вони з ситости дому Твого напо́юються, і Ти їх напува́єш з потока Своїх солодо́щів,
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
бо в Тебе джере́ло життя, в Твоїм світлі побачимо світло!
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
Продовж Свою милість на тих, хто знає Тебе, а правду Свою — на людей щиросердих!
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
Нога пи́шних нехай не наступить на мене, і безбожна рука нехай не викидає мене!
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
Попа́дали там беззако́нники, пова́лено їх — і встати не змо́жуть.

< Zabura 36 >